Connect with us

Uncategorized

Ba Mu Gama Da Siyasa Ba Tukunna, Muna Nan Dawo Wa A Shekarar 2023 – Shehu Sani

Published

on

at

Advertisement

Tsohon Sanata da ya wakilci Kaduna ta tsakiya a majalisar dattijai, Sanata Shehu Sani a ranar Laraba ya yi alfahari da cewa bai janye daga siyasa, yana nan dawo nan da shekarar 2023.

Advertisement
Advertisement

Shehu ya bayyana hakan ne a gidansa da ke Kaduna lokacin da kungiyar Magabata na Sabon Garin Nassarawa suka ba shi wata kyautar lambar yabo don kyakyawan aikinsa da kuma halin karimci ga wakilcin al’umma.

Advertisement

Naija News Hausa ta tuno da cewa Sanata Shehu Sani ya rasa kujera ta Sanata ne ga Sanata Uba Sani, wani na hannun dama ga gwamnan jihar Kaduna, Nasir El Rufai, a zaben 2019.

Advertisement
Advertisement

A lokacin ne gwamna El Rufai ya yi alfahari da cewa shan kayen Shehu Sani na nufin cewa ya yi ritaya daga siyasa, bashi ba siyasa kuma.

Advertisement

Amma da wannan zance na Shehu Sani, mai cewa “Ba mu gama da siyasa ba tukunna, za mu ko dawo”. wannan zancen tayi hannun riga da alfaharin gwamna El-rufai.

Advertisement

A cewar Shehu, “bamu da fargaba ga komai, kuma babu abinda da zai tsoratar damu daga shiga takara a 2023. Lokacin da mutanenmu suka nemi mu dawo, zamu koma”.

Advertisement
Advertisement

A yayin nuna godiya da kyautar karramawar, Shehu Sani ya ce ya yi alfahari da shugabancin aiki a Majalisar Wakilai ta kasa, kuma kyautar da aka ba shi “shaida ce ta ingancin wakilcinsa” a zaman dan majalisar dattijai a babban majalisa na 8.

Advertisement

“Majalisa na 8 sun sami damar kare mutuncin majalisar dokoki da ‘yancinsu kuma sun dage kan kare dimokiradiyya; bincike kan amfani da iko, zartarwa da aiwatar da su kan tsarin mulki da aikinsu ba tare da tsoro ko neman alfarma ba” inji shi.

Advertisement

Naija News Hausa ta ruwaito a baya da cewa Sanata mai wakiltcin Gombe ta tsakiya a majalisar dattijan Najeriya, Muhammad Danjuma Goje, ya sanar da aniyarsa na janyewa daga kara tsayawa takara a nan gaba.

Advertisement
Advertisement

Tsohon gwamnan jihar Gombe din ya bayyana hakan ne a yayin wata hidima mai taken ‘Goje Empowerment Programme’ wadda ya gudana a filin wasa na Pantami a Gombe.

Advertisement
Advertisement

Duk da haka, Goje ya ce zai ci gaba da taka rawar gani a fagen siyasar jiha da na kasa baki daya.

Advertisement