Connect with us

Labaran Najeriya

Neman karagar mulki Ga Buhari A 2023 Zai Yi Sakamako Zubar Da Jini A kasar – Annabi Josiah

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Shugaban Ikilisiyar Christ Foundation Miracle International Chapel, jihar Legas, Annabi Josiah Chukwuma ya bayyana wasu wahayin ban mamaki game da shugabancin Najeriya a 2023.

Malamin a cikin annabcin sa ya yi gargadin cewa duk wani yunkuri na Shugaba Muhammadu Buhari na neman wa’adi na uku a karagar mulki nan da 2023 zai yi sakamako zubar da jini a kasar.

Naija News Hausa ta ruwaito a baya da cewa Tsohon gwamnan jihar Anambra, Jim Nwobodo ya bayyana cewa bai dace ‘yan siyasa su fara fada kan yankin da ta dace da shugabancin Najeriya a shekarar 2023 tun yanzu.

Nwobodo, wanda ya mallaki kujerar gwamnan jihar Anambra a lokacin jamhuriya ta biyu, ya bukaci ‘yan siyasa da su kyale Shugaba Muhammadu Buhari ya mayar da hankali kan mulkin kasar a yanzu.