Connect with us

Uncategorized

Kotu Ta Ba Da Hukuncin Karshe Kan Zargin Cin Hanci Da Rashawa Ga Gwamna Ganduje

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Kotun Tarayya da ke zaune a Kano ta yi watsi da wata kara da wani lauya a Kano, Bulama Bukarti ya shigar a gabanta na neman umarnin kotun da ta tilasta wa Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arziki Kasa Ta’annati (EFCC) don ta binciki gwamna Abdullahi Ganduje bisa zargin karbar cin hancin daga hannun wani dan kwangila.

Kamfanin dillancin labarai na Naija News ta ba da rahoton cewa babbar kotun tarayya da ke zamanta a Kano, arewacin Najeriya, ta yi watsi da karar a ranar Litinin da yamma, 16 ga Disamba saboda “rashin hujja”.

Naija News Hausa ta ruwaito a baya da cewa Alhaji Aminu Ado Bayero, Sarkin Bichi a jihar Kano, Arewacin Najeriya, ya kori Shugabannin Gundumomi guda biyar a yankin nasa.

An bayyana da cewa matakin Alhaji Aminu kan cire Shugabannin Gundumomi biyar din ya faru ne saboda rashin biyayya ga Sarki Aminu Ado Bayero da masarauta bi da bi.