Connect with us

Uncategorized

‘Yan Bindiga Sanye Da Kayan Sojoji Sun Sace Yara Uku Na Mista Obi a Jihar Kaduna

Published

on

at

Advertisement

Mugun yanayi ya sanya wani dan kasuwa a Kaduna, Christian Obi kuka da hawaye a ranar Alhamis bayan da wasu ‘yan bindiga sun sace yaransa uku.

Advertisement
Advertisement

Mutumin yayin da yake zantawa da manema labarai a gidansa da ke Sabon Tasha, Kaduna, ya ce ya ga wadanda suka sace yaran ne sanye da kayan sojoji a cikin gidansa amma sai ya shiga buya.

Advertisement

Dan kasuwan ya lura cewa ya ga yadda barayin suka kwashe yaransa uku zuwa wani wurin da bai san da shi ba amma ya kasa magana don tsoron kada a kashe shi ko kuma a tafi da shi.

Advertisement
Advertisement

“Nan da nan da na hange su ta cikin gilashin gida na, na san cewa su sojoji ne na karya. Na je in ɓoye wani wuri a cikin gidana amma na ci gaba da bin matakansu. Na ga suna kwashe ‘ya’yana uku. Na kasa iya daga murya, amma a cikina, na kasance cikin hawaye da bacin zuciya” inji Mista Obi.

Advertisement

Mutumin wanda ya yi rayuwansa a Kaduna da tsawon shekaru 38 ya ce yaran da aka sace sun hada da Jonathan  dan shekara (31), Joachim (28) da kuma Benjamin mai shekaru (21).

Advertisement

Ya kuma kara da cewa har yanzu ‘Yan Bindigar ba su yi kira ba tukuna don gabatar da bukatarsu.

Advertisement
Advertisement

Wani shaidan gani da ido wanda ta bukaci kada a bayyana sunan nata ta ce ta samun ganin yadda abin ya gudana a yayin da ita ma ke a boye.

Advertisement

“Na ga maza uku, biyu na sanye da kayan sojoji kuma na ji suna magana da harshen Hausa.”

Advertisement

“Sun fada gidan ne ta yin tsalle kan shingen gidan. Daya daga cikin abokaina ne ya lura lokacin da wani a cikin su ya yi tsalle a cikin gidan, A yayin da wani shima ya bi baya.

Advertisement
Advertisement

“Suna ta zagayen gidan da neman hanyar shiga gidan amma sun kasa.”

Advertisement

“Daga dakin wanki ne suka samu yin tsalle da shiga cikin gidan ta wani karamin wuri a kofar, dukkan mu kuwa muka gudu da shiga dakin ‘yan mata don boyewa.”

Advertisement

“Lokacin da suka shigo, Jonathan ya gaya masu duk abin da suke so zai ba su. Ya ba su kudi kuma sun karɓa, duk hadi da wayoyinsu amma na samu ɓoye nawa,” in ji ta.

Advertisement
Advertisement

Kakakin Rundunar ’Yan sandan Jihar Kaduna, Yakubu Sabo ya ce ya na sane da yanayin).

Advertisement
Advertisement

“Ee muna sane da satar Ni. Ina kan aiki tukuru kan lamarin, kuma za a sanar da hakan ba ba da jimawa ba.

Advertisement