Connect with us

Labaran Najeriya

Shugabancin Kasa tayi Magana kan Zancen Buhari na Kafa Dokar Tsawan Shekaru 6 kacal a Mulki

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Fadar shugaban kasa ta musanta rade-radin cewa Shugaba Muhammadu Buhari ne ke bayan kudurin dokar shekaru shida kacal sau daya a karagar mulki wadda Majalisar Dattawa tayi watsi da ita.

Rahotanni sun bayyana cewa dan majalisar da ke daukar nauyin kudurin ya kawo hakan ne don taimaka wa shugaba Buhari ga tabbatar da wa’adin mulki na uku.

Naija News Hausa ta ruwaito a baya da cewa Shugaban kungiyar Arewa Youths Consultative Forum (AYCF), Yerima Shettima, ya yi kakkausar suka kan duk wani yunƙuri na tsawaita wa’adin Shugaba Muhammadu Buhari zuwa 2023.

Yerima ya fitar da hakan ne a bayan wata rahoton cewa, wasu gungun jama’a sun yi kira ga Shugaba Buhari da ya tsawaita wa’adin shugabancinsa zuwa shekara hudu bayan wannan wa’adin.

Haka kazalika, lauyan kundin tsarin mulki da yaki da yancin bil adama, Femi Falana (SAN) ya zargi Shugaba Buhari da shirya makircin wa’adi na uku a 2023.

A wata hirar da Shettima ya yi da manema labaran kamfanin dilancin labarai ta Daily Post, ya yi gargadin cewa za a watsar da matasan Arewa don tabbatar da dakatar da wannan yunkuri da gwamnatin a yanzu ke kokarin gabatarwa na wa’adi na uku.

“duk wani yunkuri na ci gaba da mulkin Buhari, zai sha kaye ne kamar irin ta tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo,” inji Shettima.