Connect with us

Uncategorized

Oshiomhole Ya Ki Karban kyaututtukan Kirsimeti Daga Obaseki

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Shugaban jam’iyyar APC na kasa baki daya kuma tsohon gwamnan jihar Edo, Comrade Adams Oshiomhole, ya yi watsi da kyaututtukan Kirsimeti da gwamnatin jihar Edo ta aika masa.

Mista Crusoe Osage, mai ba bada shawarwari ga gwamnan jihar Edo kan harkokin yada labarai da sadarwa, ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa a Benin a ranar Laraba.

Naija News ta ruwaito a baya da cewa Adams Oshiomhole, ya dage kan ci gaba da wata zagayen Rali da suka shirya yi a jihar Edo.

Manyan membobin jam’iyyar APC daga Abuja sun shirya da halartar taron gangamin don marabtan tsohon dan takarar gwamna Fasto Osagie Ize-Iyamu da daruruwan magoya bayansa, daga jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) a tasu jam’iyyar.

Kodashike, Mataimakin gwamnan jihar, Philip Shuaibu ya wallafa wata wasika ga Sufeto Janar na ‘yan sanda (IGP), Mohammed Adamu, da neman ya dakatar da zanga-zangar saboda hakan na iya haifar da tashin hankali a yankin.