Connect with us

Labaran Najeriya

Gwamnatin Shugaba Buhari Ta Ce El-Rufai Ne Kawai Zai Iya Yanke hukuncin El-Zakzaky

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Gwamnatin Tarayyar Najeriya a karkashin shugabancin shugaba Muhammadu Buhari ta bayyana cewa sakin jagoran Harkar Musulunci ta Najeriya (IMN) Ibrahim El-Zakzaky, ya dogara ne kawai ga gwamnatin jihar da yanke hukunci.

Naija News Hausa ta fahimta da cewa wakilan IMN, wanda kuma aka sani da Shi’a, sun yi kira da a sakin El-Zakzaky bayan sakin Sambo Dasuki da Omoyele Sowore.

Da ake mayar da martani ga bukata da binciken da jaridara The Nation ta yi, Babban Lauyan Tarayya kuma Ministan Shari’a Abubakar Malami, ya fitar a wata sanarwa daga mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Dakta Umar Jibrilu Gwandu, ya ce ana kokarin gurfanar da El-Zakzaki ne a karkashin dokar jihar Kaduna ba ta karkashin tarayya ba.

Malami ya bayyana cewa shari’ar El-Zakzaky tana da bambanci da na Sowore da Dasuki.

Bayanin Malami na kamar haka:

“A kayyade ikon da ke da alhakin bin umarnin kotu da takamaiman batun beli, dole ne a fahimci doka wanda ke jagorantar wanda ake tuhumarsa da bayar da belin shi.”

“A hannu daya kuma, inda ake tuhumar wanda ake zargi a karkashin dokar jiha, umarnin da kotu ta bayar da belin mutumin da ake tuhuma ana yin sa ne a wajen hukumomin jihar don bin doka.”

“A gefe guda kuma, inda aka gurfanar da tuhume-tuhumen a karkashin laifukan tarayya, ana bayar da umarnin bayar da belin ne a hukumomin tarayya don bin doka.”