Connect with us

Labaran Najeriya

‘Yancin El-Zakzaky Baya A Hannun El-Rufai Yake ba – IMN Sun fada wa Gwamnatin Buhari

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Kungiyar Islamic Movement of Nigeria (IMN), wacce kuma aka fi sani da suna Shi’a, ta yi Allah wadai da bayanin gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari na cewa ‘yancin shugabanta, Ibrahim El-Zakzaky ya dangana ne a hannun gwamna Nasir El-Rufai na Kaduna.

Naija News ta tuno cewa yan Shi’a sun yi kiran a saki El-Zakzaky ne bayan sakin Sambo Dasuki da Omoyele Sowore.

Amma a wata sanarwa da Gwamnatin Tarayyar Najeriya a karkashin shugabancin shugaba Muhammadu Buhari ta bayar, suna mai cewa sakin jagoran Harkar Musulunci ta Najeriya (IMN) Ibrahim El-Zakzaky, ya dogara ne kawai ga gwamnatin jihar Kaduna.

Naija News Hausa ta ruwaito a baya da cewa wakilan Harkar Musulunci a Najeriya (IMN), wadanda aka fi sani da Shi’a a ranar Laraba da ta gabata sun halarci hidimar coci ta Kirsimeti a wasu sassan arewacin Najeriya.

A cocin daban daban na Advent, Samaru, Zariya, jim kadan bayan kammala hidimar, shugaban kungiyar, Farfesa Isa Hassan-Mshelgaru ya ce muhinmancin halartar wannan hidimar shine inganta soyayya, hakuri da fahimta a tsakanin yan Najeriya.