Connect with us

Uncategorized

Gwamna Ganduje Ya Nada Mata Mataimaka na Musamman Guda 5 A Kano

Published

on

at

Advertisement

Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Ganduje ya gabatar da nadin wasu mata Biyar a Kano

Wata tsohuwar Kwamishina mai kula da harkokin mata, Hajiya Hajiya Yardada Maikano Bichi, tana daga cikin mata biyar na Musamman Mataimaka, wadanda gwamnan jihar Kano, Dokta Abdullahi Umar Ganduje ya nada.

Advertisement
Advertisement

Gwamna Ganduje bayan nadin dukkansu da kuma bayar da umarnin su fara aiki nan take, ya umarci dukkan wadanda aka nada da su tabbatar da kwarewarsu yayin aiwatar da ayukansu a kowane ofishi.

Advertisement

A cewarsa, “tunda aka zabe ku a cikin jerin mutane da yawa, ya nuna a fili da cewa muna tabbatar wa jihar da cewa kuna da abin da zai kawo ci gaban jihar.”

Advertisement
Advertisement

“Ya kamata ku tabbatar da cewa kun bi dukkanin manufofin gwamnati da shirye-shiryen da suka danganci ofisoshinku, har ma da hakan, kuna kulawa da su da dukkan hankali.”

Advertisement
Advertisement

Wadanda aka nada sun hada da, Hajiya Fatima Abdullahi Dala, a matsayin mai ba da shawara ta musamman a shafin Kulawa ga Yara da kuma Ayukan Mata; Dokta Fauziyya Buba a matsayin mai ba da shawara ta musamman a Ma’aikatar Kiwon Lafiya; Hajiya Aishatu Jaafaru, mai ba da shawara ta musamman kan Shirin ciyar da ‘yan makaranta;  Hajiya Hama Ali Aware kuma a matsayin Mai Bada shawara na musamman akan Zuba Jarin Kasashen waje, da kuma Hajiya Yardada Maikano Bichi, a matsayin Mashawarci na Musamman kan Kungiyoyi masu zaman kansu.

Advertisement