APC/PDP: Atiku Da Asiwaju Tinubu Sun Hade A Jihar Neja

Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar a ranar Asabar da ta gabata ya gana da tsohon gwamnan jihar Legas, Bola Ahmed Tinubu.

Ka tuna da cewa Atiku shi ne dan takarar shugaban kasa a babbar jam’iyyar adawa ta Najeriya, Peoples Democratic Party (PDP) a zaben 2019, a yayin da Tinubu shine shugaban jam’iyyar All Progressives Congress (APC).

Naija News ta fahimci cewa Tinubu ya hade da Atiku a Minna, babban birnin jihar Neja ne don karbar lambar girmamawa ta jami’ar Ibrahim Badamosi Babangida, Lapai.

Rahoton da aka bayar ga Naija News ya bayyana da cewa Gwamnan jihar Neja, Sani Bello, ya marabci Tinubu ne da mukarraban sa a lokacin da suka isa jihar don hidimar.

Haka kazalika gwamnan jihar Adamawa, Ahmadu Fintiri, ya kasance mabiya bayan tsohon mataimakin shugaban kasan, Atiku.

Manyan Labarai daga Jaridun Najeriya ta ranar Litini, 16 ga Watan Disamba, Shekara ta 2019

Wadannan ne Manyan Labarai ta Jaridun Najeriya a yau Litini, 16 ga Watan Disamba, 2019

1. Shugaba Buhari Ya Taya Ajimobi Murnan Cika Shekara 70

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya taya tsohon gwamnan jihar Oyo, Abiola Ajimobi murnar cika shekara 70 da haihuwa yau, 16 ga Disamba, 2019.

Buhari a cikin wata sanarwa da ya bayar ta hannun mashawarcinsa ta musamman kan harkokin yada labarai, Femi Adesina, ya taya Abiola Ajimobi ga dimbin nasarorin da ya samu a bangarorin kamfanoni da na gwamnati.

2. Tsohon Shugaban Najeriya, IBB bai Mutu ba

Naija News Hausa ta fahimta da cewa Ibrahim Badamosi Babangida (IBB), tsohon Shugaban Najeriya bai mutu ba, kamar yadda ake yada wa.

Kamfanin dillancin labarai na Naija News ta bayar da rahoton cewa rahotanni sun bayyana a wasu sassan kafafen yada labarai na Najeriya a safiyar ranar Lahadi, inda suke nuni da cewa Tsohon Shugaban na Najeriya ya mutu amma mai magana da yawun sa ya fitar da sanarwa inda ya karyata rahoton.

Mai magana da yawun IBB, Kassim Afegbua a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadin, 15 ga Disamba, ya bayyana rahotannin mutuwar IBB da cewa “labarai ne na karya”.

3. Sharia: CAN Ta Yi Kukan Cewa A Tsige Babban Alkalin Najeriya CJN Tanko

Kungiyar Kiristocin Najeriya (CAN) ta yi Allah wadai da kiran da babban mai shari’a na Najeriya (CJN), Muhammad Tanko ya yi, na yi wa kundin tsarin mulkin kasar kwaskwarima don “karbar tallafawa wasu damuwar musulmai da kuma kafa dokar Shari’a.”

Kamfanin dillancin labarai na Naija News ta bayar da rahoton cewa Tanko Muhammad ya gabatar da wannan kudurin ne yayin da yake ayyanar taron Taro na Shekaru 20 da aka bude a Jami’ar Ahmadu Bello (ABU), Zariya a ranar Laraba da ta wuce.

4. APC/PDP: Dan Takaran Shugaban Kasa Atiku Ya Hade Da Asiwaju Tinubu A Jihar Neja

Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar a ranar Asabar da ta gabata ya gana da tsohon gwamnan jihar Legas, Bola Ahmed Tinubu.

Naija News ta fahimci cewa Tinubu ya hade da Atiku a Minna, babban birnin jihar Neja ne don karbar lambar girmamawa ta jami’ar Ibrahim Badamosi Babangida, Lapai.

Gwamnan jihar Neja, Sani Bello, ya karbi Tinubu da mukarraban sa a lokacin da suka isa wajen hidimar.

5. Mashahurin Sarkin Kudu Maso Yamma ya Saki Matarsa ‘Yar Jamaica

Oba Abdulrasheed Akanbi, Oluwo na Iwoland, ya rabu da matar sa ‘yar kasar Jamaica, Chanel Chin.

Hakan ya bayyana ne ta bakin Sakataren yada labarai na Oluwo, Ali Ibrahim a wata sanarwar da ya bayar a ranar Lahadi.

6. Rikicin APC: Obaseki Da Shuaibu Na Barazanar Murkushe Ni – Oshiomhole

Shugaban Hidimar Zabe ga jam’iyyar All Progressives Congress (APC), Comrade Adams Oshiomhole, ya zargi gwamna Godwin Obaseki da mataimakin sa, Phillip Shuaibu da yin barazanar murkushe shi.

A wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi ta hannun Babban Sakataren yada labaran sa, Simon Egbuebulem, tsohon gwamnan jihar Edo ya ce gwamna Obaseki da mataimakinsa ba su da tasirin siyasa a yankinsu domin cin zabe.

Ka samu kari da Cikakken Labaran Najeriya Ta Yau a Naija News Hausa

Wata Kungiya a Arewa Ta Bada Goyon Baya Ga Tinubu Da Ya Maye Gurbin Buhari a 2023

Jagoran jam’iyyar APC na kasa baki daya, Asiwaju Bola Tinubu ya samu goyon bayan shugabancin Najeriya a lokacin da wa’adin shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kare a shekarar 2023.

Wata kungiyar siyasa, North Eastern Youth Mobilization Congress, Kungiyar Matasan Arewa da ke Yankin Arewa Maso Gabas, ta bayyana goyon bayansu a wata sanarwa da ta fitar a karshen mako a Bauchi.

Shugaban kungiyar, Aliyu Balewa ne ya ba da sanarwar a karshen bikin rantsar da shugabannin zartarwa na kungiyar.

Balewa ya ce ya kamata shugabancin kasar ta sauya zuwa Kudu a 2023 tunda Arewa a lokacin ko ta riga tayi wa’adi biyu a jere.

Ya kara da cewa Tinubu fitaccen dan siyasa ne wanda ya ba da gudummawa sosai ga tsarin siyasar kasar, kuma ya cancanci a ba shi tikitin takarar shugaban kasa a jam’iyyar APC.

“Bisa kan adalci, ya kamata mulki ya sauya zuwa yankin kudancin kasar nan a 2023 tunda Arewa ta yi aiki wa’adi biyu a jere.” inji Balewa.

“Mun yi imanin cewa mutumin da ya fi dacewa da shugabancin kasar bayan Buhari shine jigon jam’iyyar APC na kasa, Bola Tinubu, saboda ya taka rawar gani ga nasarar Buhari a zabukan 2015 da 2019. Ya kuma ba da gudummawa sosai ga nasarar APC a cikin dukkanin ofisoshin zabe.”

Balewa ya kara da cewa “Saboda haka, ya kamata shekarar 2023 ta zama lokacin biya. Bari mu mutunta yarjejeniyar mutumin ta hanyar tallafawa Kudu don samar da shugaban kasa na gaba. Kuma Bola Tinubu shine mutumin da ya fi dacewa da wannan matsayin saboda kwarewarsa ta siyasa, cancanta, bayyanar da kishin kasa.”

Manyan Labarai daga Jaridun Najeriya ta ranar Talata, 26 ga Watan Nuwamba, Shekara ta 2019

Wadannan ne Manyan Labarai ta Jaridun Najeriya a yau Talata, 26 ga Watan Nuwamba, 2019

1. Dokar Kalaman Kiyayya da Ta Kafofin Watsa Labaru Bai da wata Daraja Ga ‘yan Najeriya – Inji Wata Kungiya

Cibiyar Kula da Kare Hakkin Bil Adama da Ilimin ‘Yan Adam, yayin da take bayyana ra’ayinta game da jita-jitar kafofin watsa labarun da kuma maganganun kalaman nuna kiyayya, an lura cewa dokar ba za ta kara wani daraja ga alumma ba.

‘Yan Kungiyoyin sun bayyana kudirin da aka gabatar a zaman wani hari kan kundin tsarin mulki da ya ba da dama ga ‘yan kasa na fadin albarkacin bakin su.

2. 2023: Mafi yawan Shugabannin Kudancin Najeriya Matsorata Ne – Fani-Kayode

Ministan zirga-zirgar jiragen sama a karkashin Gwamnatin Goodluck Jonathan, Femi Fani-Kayode, ya bayyana wasu shugabannin daga yankin Kudancin Najeriya a matsayin matsoratai.

Tsohon ministan ya bayyana hakan ne yayin da yake mayar da martani kan kalaman da mukaddashin shugaban kungiyar tuntuba ta Arewa, ACF, Alhaji Musa Liman Kwande ya yi, cewa ‘yan Arewa za su zabi kawai ne dan takarar shugaban kasa wanda asalinsa dan Arewa ne a zaben shugaban kasa na 2023, ba tare da la’akari da jam’iyyun siyasa ba.

3. Mompha Ya Saura Kulle A Cikin Kurkuku

Hukumar yaki da masu yiwa tattalin arzikin kasa ta’annati, EFCC, a ranar Litinin din nan ta gurfanar da Ismaila Mustapha, wanda ake wa lakabi da Mompha da ake zargi da cin amana da zalunci a layin yanar gizo.

Naija News ta fahimci cewa an tuhume shi da aikata laifuka 14 da suka hada da cin amana a layin yanar gizo, kamar yadda EFCC ta bayar.

4. Fadar Shugaban Kasa ta Mayar da Martani Kan Motar Daukar Kudi Na Tinubu a Zaben Shugaban Kasa

Farfesa Itse Sagay, shugaban kwamitin ba da shawara ga shugaban kasa kan yaki da cin hanci da rashawa (PACAC) ya mayar da martani kan kiraye-kirayen da ake yi na binciken Asiwaju Bola Tinubu.

Idan za ka/ki iya tunawa, akwai kiraye-kiraye da cece-kuce da ake mai yawa na Hukumar Yaki da Yi wa Tattalin Arziki Tu’annati (EFCC) don bincika wasu motar daukar kudi zuwa banki da aka gano suna shiga gidan Cif Tinubu a gabanin babban zaben na 2019 a kasar.

5. Jonathan Ya Sayar da Kujerar Gwamnan Bayelsa Zuwa Ga APC – Inji Wata Kungiya

An zargi tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan da cin amanar jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) a zaben gwamna da ya gabata a jihar Bayelsa.

Wata kungiya, Kungiyar Dattawa ta Peoples Democratic Party (PDP) ta ce ta damu matuka game da matsayin Jonathan da jam’iyyar All Progressives Congress (APC) yayin zaben da aka kamala a jihar Bayelsa.

6. Wani Lauya ya zargi Shugaba Buhari da rashin biyayya ga umarnin Kotun Koli 40 Tun daga shekarar 2015

An zargi Shugaba Muhammadu Buhari da gaza bin umarnin kotu a lokuta da dama tun bayan da ya zama shugaban Najeriya a shekarar 2015.

Kolawole Olaniyan, mai ba da shawara a fannin shari’a ga kungiyar kare hakkin bil adama ta Amnesty International, ya yi zargin cewa Shugaba Buhari ya nuna “rashin ladabi ga bin doka da take hakkin dan Adam, yin watsi da alƙalai na Najeriya a aƙalla sau 40 tun daga shekarar 2015.

7. Gwamnatin Tarayya Ta Mayar da Martani Zargin Da Amurka Keyi Ga Allen Onyema

A karshe gwamnatin Najeriya ta mayar da martani game da badakalar dala miliyan 20 da aka yiwa shugaban kamfanin Air Peace, Allen Onyema.

Naija News ta tuna cewa a ranar Juma’a, 22 ga Nuwamba, 2019, Ma’aikatar Shari’a ta Amurka ta tuhumi Onyema da yaudarar bankuna da kuma karkatar da wasu kudade.

8. Kotu Ta Umarci EFCC da Dakatar da Gurfanar da Tsohon Janar na Kwastam, Dikko

Wata Babbar Kotun Tarayya da ke babban birnin tarayya, Abuja ta nemi Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arziki Ta’annati (EFCC) da ta dakatar da tuhumar da ake wa tsohon Kwanturo Janar na Kwastam (CGC), Abdullahi Inde Dikko da laifin makircin kawar da wasu kudade yayin da yake kan ofishi.

A wata hukunci da aka yanke a ranar Litinin da ta gabata, Mai shari’a Nnamdi Dimgba ya amince da gardamar Dikko da ke cewa ba za a sake gurfanar da shi ba daga wata hukuma yayin da ya kai ga arjejeniya da Gwamnatin Tarayyar kasar, da Ministan Shari’a na Tarayya (AGF) da Darakta-Janar na Ma’aikatar Gwamnatin Jiha. (DSS) don mayar wa da gwamnati dala miliyan 8m.

9. Dino Melaye Yayi Magana Game da Kauracewa Zaben Kogi

Tsohon dan majalisar dattijai mai wakiltar mazabar Kogi ta yamma, Dino Melaye, ya mayar da martani ga zargin da ake da cewa yana da shirin kauracewa babban zaben na ranar 30 ga Nuwamba.

Naija News Hausa gane da cewa Dan takarar jam’iyyar All Democratic Party ya sha kaye a hannun dan takarar jam’iyyar All Progressives Congress, Smart Adeyemi, yayin sake zaben da aka yi wanda aka gudanar a ranar 16 ga Nuwamba kafin a bayyana zaben a matsayin wanda bai yi daidai ba.

Ka samu kari da Cikakken Labaran Najeriya ta Yau a Naija News Hausa

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta Hana EFCC, ICPC Da Kwace kadarorin ‘Yan Siyasa Da aka Kama da Cin hanci da Rashawa

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta haramtawa dukkanin hukumomin hana cin hanci da rashawa a kasar damar kwace kadarorin jami’an gwamnati da aka gane ko kuma kama da halin almundahana.

Naija News ta fahimci cewa an saki wannan umarni ne a cikin wata sabuwar doka wacce gwamnatin a yanzu ta riga ta watsar da labaran haka ga sanin al’umma.

Ka tun da cea Naija News Hausa ta ruwaito a baya da cewa an gano motar daukan kudi na shiga gidan shugaban Jam’iyyar APC, Bola Tinubu.

Hakan ya afku ne ‘yan sa’o’i kadan ga zaben shugaban kasa da ta Gidan Majalisai da aka yi a watan Fabrairun 2019.

Mazuna unguwa guda da Tinubu a Jihar jihar Legas sun gano motocin da ake zargi da daukar kudi a yayin da ake shigo da su gidan Bola Tinubu, tsohon gwamnar jihar Legas da kuma shugaban jam’iyyar APC ta tarayya.

Kalli Hoton Motocin kamar yadda aka watsar a layin Twitter tun a baya;

Bullion Van entering Bourdillon, Home of Asiwaju Bola Ahmed Tinubu.

Buhari has fought corruption to standstill. pic.twitter.com/ot8S2PJWFm

— Prof Bolanlè Esq.🗨 (@BolanleCole) February 22, 2019

Manyan Labarai daga Jaridun Najeriya ta ranar Talata, 22 ga Watan Oktoba, Shekara ta 2019

Wadannan ne Manyan Labarai ta Jaridun Najeriya a yau Talata, 22 ga Watan Oktoba, 2019

1. #RevolutionNow: Kotu ta rage Kudin Belin Sowore zuwa Naira miliyan 50

Mai shari’a Ijeoma na Babbar Kotun Tarayya da ke zaune a Abuja ta duba yanayin belin da ya shafi Omoyele Sowore da Hukumar DSS.

A yayin da take bayani a ranar Litinin, lokacin da mai gabatar da kara na zanga-zangar #RevolutionNow, Omoyele Sowore, ke neman sassauci kan yanayin belin sa, Mai shari’a Ijeoma ta ce za a iya rage belin Sowore ne zuwa miliyan 50 kawai, shi kuma Bakare zuwa miliyan N20.

2. Ngige Ya Bayyana Lokacinda Biyan mafi karancin albashi Zai Samu Tasiri

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta ce cikakken aiwatarwa da kuma biyan sabon mafi karancin albashi zai gudana ba da jinkirta ba.

Naija News ta fahimci cewa Ministan kwadago da aiki, Chris Ngige ne ya sanar da hakan yayin da yake zantawa da manema labarai kwanan nan a birnin tarayya, Abuja.

3. Benue: Gwamna Ortom Ya Gargadi Buhari Kan Makiyaya daga kasar Waje

Gwamna Samuel Ortom, Gwamnan jihar Benue ya bukaci gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari da ya nemi hanyoyin hana makiyayan kasashen waje shiga Najeriya ba bisa ka’ida ba.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a lokacin da ya kai wa Malama Wanhena Cheku ziyara, wacce makiyaya zuwa yiwa raunana a kwanakin baya da ake bawa kulawa a Asibitin Kiwon Lafiya ta Tarayya da ke Apir a Makurdi.

4. Kotu ta Ba da hukunci akan Gidan Saraki da ke a Ikoyi

Babbar Kotun Tarayya da ke zaune a Legas ta ba da umarnin amshe Mallaka biyu a Ikoyi wacce ke da liki da tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Bukola Saraki.

Mai shari’a Mohammed Liman ya ba da wannan hukuncin ne biyo bayan wani kara da Hukumar Yaki da yi wa tattalin arzikin kasa ta’annati (EFCC) ta gabatar.

5. Wanda ake zargi da Kisa, David West, zai bayyana a gaban kotu

Za a gurfanar da Gracious David West, wanda ake zargi da kisan gilla, a gaban babbar kotun jihar Ribas.

Ka tuna cewa wasu mutane da dama a jihar sun tada murya da kai tsaye kan kashe-kashen mata da ake yi Otal.

6. An rantsar da Edward Onoja a Matsayin Mataimakin Gwamnan Kogi

Anyi hidimar rantsar da Cif Edward Onoja, a ranar Litinin, 21 ga Oktoba 2019 a matsayin sabon Mataimakin Gwamnan Jihar Kogi.

Naija News ta ba da rahoton cewa ‘yan majalisar sun tantance sabon Mataimakin gwamnan wanda daga nan suka neme shi da maye gurbin tsohon mataimakin gwamnan jihar, Mista Simon Achuba.

7. Bankin duniya ta amince da bada rancen dala biliyan uku ga Najeriya

Babban bankin duniya ta amince da bukatar dala biliyan 3 da Najeriya ta nema don fadada hanyoyin rarrabar da kayan wutar lantarki a kasar.

Ministar Kudi, Zainab Ahmed, da take magana bayan amincewar wannan rancen a yayin taron bankin duniya, ta ce za a rabar da rancen ne a kashi hudu na dala miliyan 750 kowanne daga shekara mai zuwa.

8. 2023: Yadda Tinubu zai Iya samun kuri’u 20m Daga Kudu maso Yamma – Ogunlewe

Wani tsohon Ministan ayyuka, Sanata Adeseye Ogunlewe, ya ba da sanarwar cewa Asiwaju Bola Tinubu, zai iya samun yawar kuri’u miliyan 20 daga Kudu maso Yamma shi kadai idan har ya yanke shawara ya tsaya takarar shugaban kasa a shekarar 2023.

Ogunlewe a cikin karyewar alkalummansa ya ce, Tinubu na iya samun kuri’u miliyan 5 daga jihar Legas shi kadai idan ‘yan siyasa daga yankin sun sanya himma a hidimar.

Ka samu kari da Cikakken Labaran Najeriya a shafin Naija News Hausa 

Manyan Labarai daga Jaridun Najeriya ta ranar Laraba 2 ga Watan Oktoba, Shekara ta 2019

Wadannan ne Manyan Labarai ta Jaridun Najeriya a yau Laraba 2 ga Watan Oktoba, 2019

1. Yan Najeriya zasuyi ci Amfanin Wutar Lantarki mara Yankewa – inji Buhari

Shugaban kasar Najeriya, Muhammadu Buhari ya yi wa ‘yan Najeriya alkawari da tabbacin cewa kasar za ta more wadataccen wutar lantarki mai tsafta ba tare da tsawa ba a nan jin kadan.

Naija News ta fahimci cewa shugaban ya yi alƙawarin ne yayin jawabinsa a ranar ‘Yancin Kai ta shekara 59. A cewarsa, gwamnatin Najeriya a jagorancin sa na shirye don samar da isashen wutar lantarki ga jama’a.

2. Shugaba Buhari Ya Bar Abuja Don ziyarar kasar South Afirka

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya shirya da barin birnin Abuja ranar Laraba yayin da zai ziyarci kasar South Afrika da tsawon kwanaki uku.

Naija News ta fahimta da cewa ziyarar ya biyo ne bayan wasikar gayyata da shugaban South Africa, Cyril Ramaphosa ya aika wa Buhari don tattaunawa kan zamantakewar ‘yan Najeriya da ke zama a kasar.

3. Bafarawa ya zargi Tinubu da haifar da matsala a APC

Tsohon gwamnan jihar Sakkwato, Attahiru Bafarawa, ya bayyana cewa rikicin shugabancin All Progressives Congress ya afku ne sanadiyar muradin Shugaban Jam’iyyar na kasa, Bola Tinubu, da ya mallaki jam’iyyar gaba daya.

Bafarawa, yayin da yake zantawar da manema labaran Guardian ya kara da cewa “rashin gaskiya da amincin Tinubu da sauran shugabannin jam’iyyar APC” ne sanadiyar rikicin da ke afkuwa a cikin jam’iyyar.

4. Nigeria @59: Aisha Buhari ta bayyana shirinta ga Najeriya

Uwargidan shugaban kasan Najeriya, Malama Aisha Buhari, ta yi baiyana shiri da burinta ga makomar Najeriya a yayin da kasar ta cika shekaru 59 da yancin kai.

Duk da cewa matar shugaban ba ta dawo kasar ba tun lokacin da aka kammala aikin Hajji a Saudiyya, Aisha ta ce ta dage da burin bautar kasar ta hanyar taimaka wa gajiyayyu.

5. Shugaba Buhari Ya shirya da Hukunta Ma’aikatan kwastom, FIRS, da Sauransu saboda gaza ga cikar Manufa

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sake jaddada kudirin gwamnatinsa na ganin an samu ci gaba ta fanin raya Tattalin Arziki da kuma habbaka a Najeriya.

Don haka, Shugaban ya ce hukumomin da ke samar da kudade ga gwamnatin za su kasance cikin sahihan bincike a nan gaba.

6. INEC ta fitar da sunayen ‘yan takarar ga zaben Gwamnonin Bayelsa

Hukumar gudanar da Zaben kasa, INEC ta fitar da jerin sunayen ‘yan takarar karshe da aka tantance wadanda za su fafata a zaben gwamna na jihar Bayelsa.

An bayar da Jerin sunayen ne a kunshe cikin wata sanarwa a ranar Talata wanda Naija News ta samu daga layin Twitter na INEC.

7. Najeriya A 59: Kalubalen Najeriya Matsaloli ne mai kai mu ga Nasara – in ji Lawan

Shugaban majalisar dattijai, Ahmed Lawan, ya ce kalubalen da Najeriya ke fuskanta matsaloli ne da zasu kai kasar ga cin nasara ta musanman.

Naija News ta fahimci cewa Shugaban Majalisar Dattawar ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ya yi don bikin ranar samun ‘yancin kai na Najeriya ta shekara 59.

8. Najeriya A 59: Dalilin da yasa Na kafa Majalisar Ba da Shawara kan Tattalin Arziki – Buhari

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bayyana cewa ya kafa sabon kwamitin ba da shawara kan tattalin arziki (EAC) ne domin su yi ta yi masa nasiha game da manufofin kasafin kudin kasar.

Wannan bayanin shugaba Buhari ya fito ne a ranar Talata yayin watsa jawabinsa lokacin bikin ‘yancin kai ga ‘yan Najeriya.

9. Shugaba Buhari Ya Ba da umarnin Sakin N600bn Domin Ayyuka ga Kasar

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya umarci Ministar Kudi, Misis Zainab Ahmed da ta saki naira biliyan N600 domin kashe kudaden ga manyan ayuka a kasar a cikin watanni uku masu gabatowa.

Naija News ta fahimci cewa an ba da wannan umarni ne a yayin sakon tunawa da shekaru 59 na ‘yancin kai ga ‘yan Najeriya a ranar Talata a birnin tarayya, Abuja.

Ka samu kari da Cikakken Labaran Najeriya ta yau a shafin Naija News Hausa

Ina Kuwa Tausaya wa Tinubu – Mike Ozekhome

Babban Lauyan fafutukar Kasa, Mista Mike Ozekhome, ya bayyana cewa yana tausayawa Shugaban jam’iyyar APC, Bola Tinubu.

Mike, Mai kare hakkin dan adam ya bayyana cewa rukunonin da ke a cikin gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari suna shirin tsige Mataimakin Shugaban kasa, Yemi Osinbajo ne, bayan da suka yaudare shi da amfani da shi wajen rarraba Tradermoni ga ‘yan kasuwa kamin babban zaben da ya gabata.

Wannan furci ta Mike Ozekhome na fitowa ne bayan wasu cece-kuce da ya biyo matakin da shugaba Muhammadu Buhari da Gwamnatinsa ta dauka na raba Osinbajo da wasu makamai da ya jagoranta.

Ka tuna, kamar yada Naija News Hausa ta ruwaito a baya da cewa Shugaba Muhammadu Buhari ya bayyana murnan sa da irin abokin takara da ya ke da shi, watau hadewarsa da Farfesa Yemi Osinbajo.

Naija News Hausa gane da bayanin Buhari ne a yayin bayan hadarin jirgin sama da Farfesa Yemi Osibanjo ya yi a ranar 2 ga Watan Fabrairu, 2019 a lokacin da yake hanyar zuwa Jihar Kogi don gudanar da yakin neman zabe a Jihar.

“Na Gode wa Allah da kare mataimaki na, Farfesa Yemi Osibanjo daga hadarin jirgin sama da ya yi a ranar Asabar da ta gabata,”

“Ina yaba wa mataimaki na da kuzari, kokari da kuma irin karfin lamirin zuciya da ya ke da shi, harma da iya ci gaba da hidimar yakin neman zaben bayan hadarin da ya faru da shi a ranar” in ji fadin Buhari.

Manyan Labarai daga Jaridun Najeriya ta ranar Talata, 13 ga Watan Agusta, Shekara ta 2019

Wadannan ne Manyan Labarai ta Jaridun Najeriya a yau Talata, 13 ga Watan Agusta, 2019

1. Gwamnatin Tarayya ta ba da Dalilin da yasa ba ta aiwatar da biyan kankanin Albashi ba

Bayan barazanar shiga zanga-zanga da kungiyar kwadago ta yi, Gwamnatin Tarayya ta danganta jinkirin aiwatar da sabon albashi mafi karancin ga Ma’aikata da sanadiyar wasu bukatu marasa manufa da kungiyar kwadago ta gabatar.

An bayyana wannan zancen ne a bakin, Richard Egbule, Shugaban Hukumar Albashi ta Kasa, da Hukumar Inshorar a yayin wata tattaunawa da yayi da NAN a ranar Litinin da ta wuce.

2. Shugabancin Kasa ta Bayyana Abinda Shugaba Buhari keyi Game da Rikicin Sojoji da ‘Yan Sanda

Shugabancin kasar ta bayyana da cewa akasin ganewa da imanin wasu a kasar na nunin cewa Shugaba Muhammadu Buhari bai damu da rikicin da ya afku tsakanin jami’an ‘yan sanda da sojoji ba.

Ka tuna kamar yadda Naija News ta sanar a baya da cewa darukan sojojin Najeriya sun kashe wasu jami’an ‘yan sanda a jihar Taraba wadanda ke biye da wani jagoran ‘yan fashi, Alhaji Hamisu.

3. El-Zakzaky da Matar sa sun tashi daga Najeriya zuwa kasar Turai

Shugaban kungiyar Harkar Musulunci ta Najeriya (IMN), wanda aka fi sani da ‘Yan Shi’a, Shaikh Ibraheem El-Zakzaky da matarsa, Zeenat, a daren ranar Litinin din nan, sun bar kasar zuwa Indiya don binciken lafiyar jikinsu.

Naija News Hausa ta fahimta da cewa sun tashi zuwa India ne a kan jirgin Emirate daga filin jirgin sama ta Nnamdi Azikiwe da ke Abuja.

4. Dalilin da yasa ya zan dole ga EFCC ta Kama Buhari da Tinubu – Omokri

Reno Omokri, tsohon mai mataimaki ga hidimar aiki ga tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan, ya ce ikirarin da Timi Frank ya bayar ya tabbatar da cewa ya karyata Jonathan.

Ya kara da cewa furucin Frank, tsohon Sakataren yada labarai na Jam’iyyar APC na kasa ya tabbatar da cewa tsohon Shugaba Jonathan mai Imani ne.

5. Abinda ya zan Dole da yi ga ‘Yan Najeriya  – Bola Tinubu

Jagoran jam’iyyar APC na kasa baki daya, shugaba Bola Tinubu, ya ce dole ne ‘yan Najeriya su sadaukar da kansu ga ci gaba da karuwar kasar.

Naija News ta gane da cewa Tinubu yayi wannan tsokaci ne yayin da yake zantawa da manema labarai bayan kammala sallar Eid-el-Kabir.

6. Abin da Shugaban Guinea ya fada wa Buhari game da Tinubu

Naija News Hausa ta fahimta bisa rahotannai da cewa daya daga cikin dalilin ziyarar shugaban kasar Guinea, Shugaba Alpha Conde ga Buhari ita ce neman dama ga Cif Bola Tinubu don maye gurbin Shugaba Muhammadu Buhari a shekarar 2023.

Ka tuna da cewa Conde ya halara a garin Daura na jihar Katsina a karshen mako don ziyarar shugaba Buhari yayin da shugabannin kasashen Afirka biyu ke bikin zagayowar Sallar Eid-El-Kabir.

7. Rundunar Sojojin Najeriya ta Kori wani Jarumi don Lalata da wata Daliba Jami’a

Sunday Adelola, mai igiyar daukaka ta Lance Corporal ta sojojin Najeriya wanda aka kama da yi wa wata daliba makarantar Jami’a ta Adekunle Ajasin Akungba Akoko fyaden Dole.

Naija News ta fahimci cewa an mika Mista Adelola ga ‘yan sanda don bincike tare da gurfanar da shi nan take rundunar ta kore shi.

8. Kungiyar Kwadago ta Najeriya ta gabatar da sabon gargadu  ga Gwamnati

Kungiyar kwadago ta kasa (TUC) ta gargadi gwamnatin tarayya da ta daina jinkiri da biyan sabon albashi mafi karanci ga Albashin ma’aikatan Najeriya.

Shugaban TUC na jihar Ekiti, Sola Adigun, wanda ya yi wannan kiran, ya roki Gwamnatin Tarayya da kar ta kara ga jinkirtar biyan albashin, da kuma kada su wuce ranar Laraba, 14 ga Agusta 2019.

Ka samu kari da cikakken Labaran Najeriya a shafin NaijaNewsHausa

Manyan Labarai daga Jaridun Najeriya ta ranar Jumma’a, 28 ga Watan Yuni, Shekara ta 2019

Wadannan ne Manyan Labarai ta Jaridun Najeriya a yau Jumma’a, 28 ga Watan Yuni, 2019

1. Shugaba Buhari ya rantsar da Ciyaman na Hukumar RMAFC

A ranar Alhamis da ta gabata, Shugaba Muhammadu Buhari ya rantsar da Mista Elias Mbam, a matsayin ciyaman na Hukumar Karba da tsarafar da Ravanu ta kasa (RMAFC).

Shugaban ya kuma rantsar da Kwamishanoni 30 ga hukumar, a ganewar Naija News Hausa.

2. Shugaba Buhari ya bayyana lokacin da za a fara biyan kankanin Albashin Ma’aikata

Shugaba Muhammadu Buhari a ranar Alhamis da ta wuce, ya bada haske ga gurin gwamnatinsa wajen tabbatar da fara biyan sabon tsarin kankanin albashin ma’aikata na dubu talatin (30,000), kamar yadda aka amince da ita a baya.

Shugaban ya kuma gargadi gwamnonin Jiha da jiha hade da shugabannan kamfanoni da tabbatar da adalci wajen biyan albashin da ya dace ga ma’aikatansu.

3. Ba dole bane sai Dalibi yayi hidimar Bautan kasa (NYSC) kamin ya shiga takaran Gwamna – Kotu ta fadi haka

Kotun Koli ta birnin Tarayyar Najeriya (FCT) ta nuna watsi da zancen cewa duk dalibin da ya kamala karatun jami’a da kuma bai je hidimar bautar kasa (NYSC) bai da damar shiga takara da neman kujerar gwamna.

Kotun ta furta hakan ne bisa wata karar zargi da aka gabatar a gaban kotun akan Gwamnan Jihar Ogun, Dapo Abiodun, daga hannun tsohon Sanata, Iyabo Anisulowo.

4. Kotun Kara ta yi watsi da rubutacciyar ƙara game da Buhari

A ranar Labara da ta gabata, kotun hukunci ga karar zaben kasar Najeriya ta gabatar da yin watsi da wata rubutacciyar ƙara da aka mika a gaban kotun, na neman janyewar Jam’iyyar Hope Democratic Party (HDP) daga zancen kalubalantar shugaba Muhammadu Buhari ga zaben 2019.

Naija News Hausa ta gane da hakan ne bisa bayanin Alkali Mohammed Garba, a yayin da yake gabatarwa game da karar zaben shugaban kasa ta 23 ga watan Fabrairu da ta gabata.

5. Amaechi ya tada murya ga bayyana masu kokarin lalatar da adalcinsa

Tsohon Ministan harkokin sufuri, Hon. Rotimi Amaechi, ya gabatar da zargin cewa wasu na neman bata masa suna a kasar.

A wata sanarwa da aka bayar ga Naija News a ranar Alhamis da ta gabata daga hannun rukunin sadar da labarai ga Amaechi, ya bayyana da cewa kokarin ‘yan neman shugabanci kotayaya na kokarin su lalatar da sunansa da kuma adalcinsa.

6. Kotu ta daga ranar Hukunci ga Karar da aka gabatar game da Ganduje

Alkali Ahmed Tijjani Badamosi da ke a Kotun Koli ta Jihar Kano, ya dagarda hukuncin karar da masu nadin sarautan Jihar Kano suka gabatar a kotun akan matakin Gwamna Abdullahi Ganduje na kara sabbin kujerar sarauta hudu ga Jihar a baya.

Naija News Hausa ta ruwaito a baya da cewa Gwamnan Kano ya kara kujerar Sarauta Hudu a Jihar Kano.

7. Shugabanci kasar Najeriya na shirin sanya sabbin Ministoci

Hukumomin Tsaron kasar Najeriya sun fara shirin bada sunayan wadanda zasu yi rikon kujerar Minista a hukumomin daga Jihohi daban daban.

Naija News ta fahimta da cewa an fara wannan shiri ne kamin shugaba Muhammadu Buhari ya gabatar da masu jagoranci a rukunin shugabancin sa ta karo biyu.

8. Dalilin da yasa Buhari ba zai iya bayar da shugabanci ga Tinubu ba – Adebanjo

Shugaban Hadadiyar Kungiyar Zamantakewar Al’adar Yarbawa da aka fi sani da Afenifere, Mista Ayo Adebanjo ya kalubalanci shugaban tarayyar Jam’iyyar APC, Bola Tinubu da wasu manya daga Yarbawan kasar da yaudarar shugaba Muhammadu Buhari a diban cewa suna murna da shugabancin sa.

“Suna yaudaran shugaban ne don don watakila zai bayar da daman neman shugabancin kasar ga Kudu maso yammacin kasar a shekarar 2023.

9. Ka bada shaidar cewa na sace Motoci 67  – Okorocha ya kalubalanci Ihedioha

Tsohon Gwamnan Jihar Imo, Sanata Rochas Okorocha ya kalubalanci sabon gwamnan Jihar da ya maye gurbinsa, Emeka Ihedioha da cewa ya bayyanar da shaidan tabbacin zargin da yake a gareshi na sace motocin jihar guda 67.

Okorocha ya kuma bada tsawon kwanaki bakwai ga Ihedioha don gabatar da shaidarsa akan zargin.

Ka samu kari da cikakken Labaran Najeriya a shafin Hausa.NaijaNews.Com