Dan Majalisar Wakilai a Jihar Kwara, Saidu Rufai Ya Mutu

A cewar wata rahoto da aka bayar daga kamfanin dilancin labarai ta Vanguard, dan majalisar wakilai a jihar Kwara, wanda ke wakilcin mazabar Patigi a zauren majalisar dokoki na 9 na jihar Kwara, Hon. Ahmed Saidu Rufai ya mutu.

Wannan sanarwan ya fito ne a kunshe a cikin sanarwar manema labarai wanda Mataimakin Musamman a kafofin watsa labarai ga dan majalisar, kakakin yada yawun majalisar Wakilai ta Jihar Kwara, Rt. Hon. Salihu Yakubu Danladi ya bayar.

Sanarwar ta ce;

“Hadi da matukar raha tare da mika wuya ga yardar Allah Madaukakin Sarki, muna sanar da rasuwar abokin aikinmu, Hon. Ahmed Saidu Rufai mai wakiltar mazabar Patigi ”.

“Wannan wani lamari ce wanda bamu zata ba da kuma ya jefa mu cikin wani mummunan hali, amma abin takaici, Madaukakin Sarki ya hana mu ikon juya irin wannan lamari da ya faru”, in ji Danladi.

“Yayin da muke kokawa da rayuwa tare da wannan mummunan al’amari da kuma yanayin da ake a ciki, muna rokon Allah cikin rahamarSa ya gafarta masa kurakuran sa, ya baiwa iyalan sa, majalisa ta 9, Patigi Emirate, abokan arziki na tarayya kuma da jihar Kwara baki daya, ƙarfin yin hakuri da amince da wannan al’amari da ya riga ya faru.”

Naija News Hausa ta fahimta da cewa Hon. Ahmed Saidu Rufai ya mutu ne a asibitin koyarwa na jami’ar Ilorin da safiyar yau kuma za a yi hidimar Jannazah na marigayin dan majalisar ne a yau jim kadam a harabar gidansu da ke a Patigi.

Gwamnan Jihar Kwara ya gabatar da Matashiya mai shekara 26 a matsayin Kwamishina

Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq na jihar Kwara, ya nada Miss Joana Nnazua Kolo, mace mai shekaru 26 da haihuwa da ke hidimar bautar kasa (NYSC), a matsayin kwamishina.

Naija News ta ba da rahoton cewa Matashiyar mai shekaru 26 na daga cikin kwamishinoni mata hudu wadanda aka zaba da mika sunayensu ga majalisar dokokin jihar Kwara a ranar Talata, 17 ga Satumbar don tantancewa.

Kolo, ƙaramar yarinya a tarihin jihar, zabbbiya a cikin jerin sunayan kwamishinoni, ta kammala karatun digiri dinta ne a Makarantar Kimiyya ta Jami’ar Kwara (KWASU), ƙwararrace kuma wajen fafutukar ci gaban al’umma.

Idan har aka tabbatar da ita daga Majalisa a matsayin, za ta zama kwamishina mafi karancin shekaru a Najeriya, zata kuwa dauki matsayin karancin shekaru daga Oluwaseun Fakorede, Kwamishana mai shekaru 27 a jihar Oyo.

Naija News Hausa nada sanin cewa Kolo har yanzu tana cikin hidimarta na bautar kasar, watau “National Youths Service Corps” NYSC a Jigawa, inda take koyarwa a Makarantar Sakandare ta Model Boarding Secondary School Guri.

Za’a kuwa gudanar da nata binciken ne akan kujerar majalisar minista bayan da ta kammala hidimar NYSC dinta a makonni biyu da ke gabatowa.

 

Manyan Labarai daga Jaridun Najeriya ta ranar Jumma’a, 16 ga Watan Agusta, Shekara ta 2019

Wadannan ne Manyan Labarai ta Jaridun Najeriya a yau Jumma’a, 16 ga Watan Agusta, 2019

1. El-Zakzaky da Matarsa sun kamo hanyar dawowa Najeriya

Ibraheem El-Zakzaky, jagoran Kungiyar Harkar ci gaban Musulunci ta Najeriya (IMN), wanda kuma aka fi sani da Shi’a da Matarsa, Zeenah Ibrahim, suna kan hanyarsu ta dawowa Najeriya daga kasar Indiya.

Naija News ta fahimci cewa su biyun za su dawo kasar ne bayan tafiyar kwana uku na ziyarar Indiya don binciken lafiyar jikinsu.

2. Kotu ta Ba da belin N20m Ga Surukin Atiku

Dakta Abdullahi Babalele, suruki ga dan takarar shugaban kasa a karkashin Jam’iyyar PDP a zaben 2019, Alhaji Atiku Abubakar, ya sami damar beli daga Kotu.

Alkali Nicholas Oweibo na babbar kotun tarayya da ke Legas ne ya bayar da belin a ranar Alhamis da ta gabata.

3. Gwamnatin Tarayya ta canza suna Na Hanyar Yanar Gizon Twitter

Gwamnatin tarayyar Najeriya a ranar Alhamis da ta wuce, ta sanar da canza da sunan shafin yanar gizon da gwamnati ke amfani da ita a layin twitter.

Naija News Hausa ta fahimci cewa a yanzu sunan ya koma @NigeriaGov, maimakon @AsoRock, kamar yada take a da.

4. Abin da Ubana ya gaya mani a Indiya – ‘Yar El-Zakzaky

Suhaila Zakzaky, ‘ya ga El-Zakzaky’ ta bayyana cewa mahaifinta na fama da gubar dalma da kuma guba ta cadmium.

Ka tuna da cewa tun da farko shugaban IMN din ya ki karbar magani daga wasu likitoci da bai san da su ba da aka sanya don yi masa magani a Indiya.

5. Jam’iyyar PDP sun kalubalanci Umarnin Shugaba Buhari zuwa ga CBN

Jam’iyyar Dimokradiyya, babbar Jam’iyyar Adawa ta Najeriya (PDP) ta bayyana umarnin shugaban kasa Muhammadu Buhari ga Babban Bankin Najeriya (CBN) kan shigo da abinci a matsayin mataki mara wadataccen tsari.

Naija News ta tuna cewa Buhari ya umarci Babban Bankin Najeriya (CBN) da ta daina ba da kudin musayar kasashen waje don shigo da abinci cikin kasar.

6. Kotun Kara ta sanya ranar yin hukunci akan Zaben Jihar Kwara

Kotun sauraren kararrakin zaben jihar Kwara ta sanya ranar Juma’a, 20 ga Satumbar, 2019, don gabatar da hukunci akan takarda kara da dan takara, Rasak Atunwa, dan jam’iyyar Dimokradiyya (PDP), ya kalubalanci nasarar gwamna AbdulRahman AbdulRazaq a zaben Gwamnonin Jihar.

Naija News ta fahimci cewa dan takarar PDP a zaben gwamna a shekarar 2019 na kalubalantar zaben AbdulRazaq a kotun bisa dalilin cewa gwamnan ya gabatar da takardar shaidar kammala makarantar sakandare ta karya wanda bai cancanta ba.

7. Shugaba Buhari ya wallafa Matakai da Manufofi kan sabbin Ministocin da ke shigowa

Shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari, ya fada da cewa Ministocin da ke shigowa zasu yi aiki ne bisa tsari da karbar umarni.

Naija News ta gane da cewa Shugaba Buhari ya sanar da hakan ne a cikin wata sanarwa da aka sanya a shafin yanar gizon Twitter, ranar Laraba, 14 ga Agusta da ta wuce da yamma.

8. Gidan Majalisar Wakilai ta yi kirar zama ga Emefiele, NNPC, shugaban DSS

A ranar Alhamis din da ta gabata ne majalisar wakilai ta yi kirar gaugawa ga  Gwamnan Babban Bankin Najeriya, Godwin Emefiele; Manajan Darakta na Kamfanin Man Fetur na Najeriya (NNPC), Mele Kyari; da Babban kwamandan Hukumar Kwastam na Najeriya, Col. Hameed Ali (retd.); da Darakta-Janar, Ayukan Jiha, Yusuf Bichi.

Naija News ta fahimci cewa an yi masu kirar zaman ne saboda gazawar su ga halartar sauraron karar da majalisar ta shirya kan matsalar tashoshin jiragen ruwa a cikin kasar.

Ka sami kari da cikakken Labaran Najeriya a shafin NaijaNews.Com

Kaito! Karanta Dalilin da yasa wani ya kashe Makwabcin sa a Jihar Kwara

Kotu Majistare ta garin Ilorin, babban Birnin Jihar Kwara, ta saka wani mutumi mai suna Umar Abubakar a gidan Maza da zargin kashe makwabcin sa Umaru Mohammed.

Naija News Hausa ta fahimta da hakan ne bayan hukuncin da Kotun ta bayar ranar Talata, 2 ga watan Yuli.

A lokacin da Ofisan ‘Yan Sanda da ke jagorancin karar, Insp. Abdullahi Sanni ke bayani game da karar a Kotu, ya bada haske da cewa an kame mutumin ne tun ranar 20 ga wata Yuni, 2019 da ta gabta da zargin kashe makwabcin sa bayan wata rashin ganewa tsakanin su.

Insfekta Sanni ya bayar ga manema labarai da cewa Abubakar ya kashe marigayin ne a yayin da suke fada don marigayin ya hana shi wasa da kanuwarsa.

“Abin ya faru ne a shiyar Banni, a karamar hukumar Kosubosu, Jihar Kwara.” inji Sanni.

“An gabatar da Abubakar a kotu ne da laifin kisa da kuma karya dokar kasa kamar yadda take a litafin dokoki, a fale ta 221 na dokar kasa”

Babban Alkali da ke wakilcin Kotun Majistare ta Ilorin, Jumoke Bamigboye, bayan da tayi binbini da zargin sai ta bada hunkuncin cewa a jefa Abubakar a gidan Jaru da ke a Okekura, garin Ilori.

A haka ta daga hukuncin karshe ga zargin da ake da Abubakar zuwa ranar 26 ga watan Yuli ta shekarar 2019.

Ciyamomin Jihar Kwara sun kai Gwamnan Jihar a Kotu

Ciyamomi 16 da gwamnatin Jihar Kwara ta gabatar da tsigewa ‘yan kwanaki da suka shige sun yi karar Gwamnan Jihar, Abdulrahman AbdulRazaq da ‘yan Majalisar Jihar zuwa Kotu.

A bayanin Ciyamomin, sun bayyana da cewa matakin gwamna Abdulrahman Abdurasak na dakatar da su ba daidai bane; “Wannan ba a kan doka bane, kuma barnan lokaci ne kawai wanda kuma bamu amince da ita ba” inji su.

Ciyaman na Kungiyar Ciyamomin kananan hukumomin Najeriya, Mista Joshua Adekanye ya gabatar da cewa akwai wata doka a kotu da ya hana irin wannan mataki ga kowane gwamnati.

Mista Joshua ya kara da cewa abin ya zan mashi da mamaki ganin gwamnan Jihar da daukan irin wannan matakin, da sanin cewa bawai sun kai ga karshen wakilcin su ba, wanda bissa ranar rantsarwa da kuma doka sai watan Nuwamba a shekara ta gaba kamin su karshe wakilcinsu.

Ko da shike, magatakardan Gwamnan, Mista Rafiu Ajakaye ya bayar da cewa gwamnan ya dauki matakin ne bisa hadin kai da amincewar majalisar jihar.

Naija News Hausa ta fahimta da cewa majalisar jihar ne ta gabatar da dakatar da ciyamomin jihar ya ga tsawon watannai shidda har su kamala wata bincike makirci da cin hanci da rashawa na kudi kimanin naira Biliyan Talatin da Uku (N33b).

KARANTA WANNAN KUMA; ‘Yan Ta’adda sun yiwa Oshiomhole da wasu ‘yan Majalisa 14 duka a Jihar Edo

Wani Mahaukaci ya Kashe Dan Sanda a Jihar Kwara

Hukumar Jami’an Tsaro ta Jihar Kwara sun gabatar da cewa wani mutumi da ake dubin shi da tabuwar kwakwalwa, ya kashe daya daga cikin ofisan tsaron su da tsaran Adda.

Bisa bayanin da hukumar ta bayar, Naija News Hausa ta gane ne da cewa mahaukacin ya hari Sgt. Abu ne da Adda a ranar Talata da ta gabata a yayin da yake kan tsaro cikin kewayan Ofishin su da ke a yankin Omu-Aran, Arewacin Jihar Kwara.

An bayyana da cewa an haura da kai Mista Abu a wata Asibitin kamin dada aka kara gaba da shi a Babban Asibitin da ake kira ‘Ido Medical Centre’ a Jihar Ekiti, a inda ya mutu a ranar Laraba da ta gabata.

A bayanin wani da ya samu ganin al’amarin, ya gayawa manema labarai a haka,  “Ina saman Babur di na ne da na ga mutumin mai Alamun tabuwar kwakwalwa yadda ya ke saran dan sandan da Adda da kuma bungun Icce”

“Na bi shi da gudu hade da wasu ‘yan kabukabu. Ya kama hanyar Taiwo da gudu muna biye da shi, ‘yan lokatai kadan sai ya tsaya, ya kuma mika hannun sa biyu a sama, da alamun saranda” inji shi

“Anan take ‘yan sanda suka biyo da kame shi, suka kuma tafi dashi a Ofishin su”

Mista Ajayi Okasanmi, Kakakin yada yawun jami’an tsaron ‘yan sandan Jihar, ya bayyana da cewa hukumar su na kan bincike akan lamarin.

Mun ruwaito a Naija News Hausa a baya da cewa Hedkwatan Rundunar Sojojin Najeriya ta ‘Operation Whirl Stroke’ (OPWS) sun ci karo da wasu mutane biyu da ake zargin su da kirar bindigogi. sun gane da hakan ne a wata zagayen bincike da suka yi a Jihar Nasarawa, Taraba da Jihar Benue.

Kalli Shawarar da Sanata Saraki ya bayar ga ‘yan Gidan Majalisar Dattijai

Tsohon Shugaban Sanatocin Najeriya, Dakta Bukola Saraki yayi kira ga ‘yan gidan Majalisa da su hada hannu don aiki tare ga ganin cewa sun daukaka kasar Najeriya wajen shugabancin su.

Naija News Hausa ta ruwaito a baya da cewa Dakta Bukola Saraki ya fadi daga tseren takaran kujerar Sanata daga Jihar Kwara.
Sanata Saraki ya shawarci ‘yan gidan Majalisar ne a yayin da yake wata gabatarwa ga sabbin shugabannin gidan Majalisar ta 9.
“Ku ci gaba da kare zumunci da girman kasar nan Najeriya a duk cikin ayukan ku” inji shugaban a wata bidiyon da ya rabas a layin yanar gizon nishadarwa ta Twitter da ya ke amfani da ita.

Sanata Saraki ya kara da cewa “Yana da muhimanci kwarai da gaske da ganin cewa kan ku na hade. An zabe ku ne daga jam’iyoyi dabam dabam, Idan ko kuna son ku cika gurin ‘yan Najeriya da suka sanya ku a kujerar mulki, dole ne jam’iyyar ku ta zama daya a cikin gidan Majalisar” inji shi.

Karanta wannan: Zaku ko tayar da Hitina, idan har kuka kame Uche Secondus, Sanata Dino ya gayawa Jam’iyyar APC

Kotu ta saka wani gidan jaru na tsawon shekaru 10 da zargin kisan kai

Kotun Koli ta Jihar Kwara ta saka wani matashi mai shekaru 21 ga kurkuku na tsaron shekaru 10 akan laifin kisan kai da ake zargin shi da ita.

Shefiu Abubakar zai lashe jarun shekaru 10 ne don kisan dan uwan sa, Babuga Abubakar da bugun itace.

Kotu ta gabatar da shiga kurkukun Shefiu ne a ranar jiya Alhamis 28 ga watan Maris 2019 a jagorancin Alkali Durosinlohun Kawu, a nan Kotun Koli ta garin Ilorin, Babban birnin Jihar Kwara.

Bincike ya nuna da cewa abin ya faru ne a shekarar 2015 da ta wuce a shiyar Dona Dogo ta karamar hukumar Edu, a Jihar Kwara. Ko da shike ba a bayyana dalilin da ya sa aka dakatar da karar har ga wannan lokaci ba, amma an sanya Shefiu da shiga jarun tsawon shekaru 10.

An bayyana ne da cewa Shefiu ya aiwatar da kisan ne da zaton cewa dan uwansa Babuga na kwanci da matar sa.

Ko da shike an fada da cewa Shefiu kamin ya aiwatar da kisan dan uwansa, ya riga yayi karar Babuga ga jami’an tsaron ‘yan sandan yankin da cewa yana zargin sa da kwanciya da matarsa.

Bayan hakan ne Shefiu ya ziyarci gidan Babuga, ya kira shi a waje, ya kuma buge shi da guntun icce, a nan take kuma Babuga ya mutu.

A halin yanzu Shefiu ya riga yayi shekaru hudu a gidan jaru tun lokacin da abin ya faru. Kotu ta bayyana da cewa zai karshe tsawon shekaru shidda don cika sabon hukunci da aka yi masa bisa kan dokar kasa da ya karya.

Kash! Ibrahim Chatta Umar ya mutu

Naija News Hausa ta samu sabon rahoto da tabbacin mutuwar Etsu Patigi, Alhaji Ibrahim Chatta Umar bayan rashin lafiyar ‘yan kwanaki kadan.

Alhaji Chatta ya mutu ne daren ranar Talata, 19 ga watan Maris da ta gabata a garin Abuja, babban birnin Tarayyar Najeriya. Za a kuma yi hidimar zana’izar sa a yau Laraba, 20 ga watan Maris 2019 missalin karfe 2 tsakar ranar yau, kamar yadda al’adar Islam ta bayar.

“Wannan babban rashi ce kwarai da gaske. Alhaji Ibrahim Chatta mutumi ne mai ban girma, kuma mutumin adalci ne shi” inji Sarkin Ilorin da kuma shugaban kungiyar Sarakunan Jihar Kwara, Alhaji (Dr) Ibrahim Sulu-Gambari.

Sarkin ya gabatar da bayanin sa ne na ta’aziyya daga bakin babban sakataren kungiyar Shehu Alimi akan zamantakewar lafiyar kasa da ci gaba, Mallam Abdulazeez Arowona, a cikin wata sanarwa da ya gabatar bayan mutuwar Chatta.

Alhaji Sulu-Gambari ya kara da cewa Chatta mutum ne mai kwanciyar hankali da kuma kadamar da shirya zamantakewar lafiya ga al’ummar Jihar, musanman ma da duk yaran Nufawa da ke Jihar Kwara.

“Mutuwar Chatta abin takaici ne kuma da bakin ciki a garemu, gurbin sa kuma zai zama a sake a  wannan lokacin” inji Alhaji Sulu.

Naija News ta gane da cewa Etsu Patigi na zaman mataimaki ne ga Sarkin Ilori, Alhaji Sulu-Gambari a shugabancin Sarakunan Jihar Kwara, kamin mutuwar sa.

“Ina rokon Allah da gafarta wa Chatta zunuban san, ya kuma sa ya kai ga shiga al-janatul firdaos, ya kuma yi ta’aziyya ga Iyalan sa da ya bari har ma mutanen Patigi hade da Nufawan kasar duka”

Wannan itace addu’ar Sarki Sulu-Gambari.

Karanta wannan kuma: Wuta kame gidaje da barin Iyalai 20 da rashin wajen kwanci da kayan zaman rayuwa

Kash: An gunce hannun wata tsohuwa a Jihar Kwara

Abin takaici, wani mai suna Lukman ya gunce hannun wata mata mai shekaru 60 a yankin Omu-Aran ta Jihar Kwara, a ranar Asabar da ta gabata.

An bayyana ga menama labarai da cewa abin ya faru ne daren ranar Asabar da ta wuce, a yayin da Lukman ya gunce wa Muibat Abifarin hannu bayan wata gardama da ta tashi tsakanin Abeeb Abifarin, yaron tsohuwar da Lukman akan zargin cewa Lukman ya gasa wata akuya.

An kara bayyana da cewa Lukman na da alamun haukacewa, a yayin da aka gane da cewa ya hari wasu mutane biyu da suke zama cikin gida guda a Orolodo, nan kusa da fadar sarkin Omu-Aran ta Jihar Kwara.

An gabatar da cewa matar, an kai Muibat a asibiti a gaggauce don karban kulawa ta gaske. sauran mutane biyu kuma da Lukman yayi wa rauni a na a nan Asibitin Tarayya ta Omo-Aran don samun kulawa ta kwarai.

“Muibat na samun isasshen kulawa, amma ba a bar kowa ya shiga ganin ta ba, sai har ta samu karin sauki a nan cikin asibitin da ta ke” inji manema labarai da ya ziyarci wajen.

“Abin ya faru ne missalin karfe 10 na daren ranar Asabar lokacin da kowa a gidan ke kokarin shiga barci. Gardama ya tashi ne tsakanin Lukman da yaya na Abeeb akan wata Akuya da Lukman ya soye. Daga nan gardaman tayi zafi har Lukman ya hari Abeeb da kokarin ya sare shi da Adda”

“Ana cikin hakan ne sai ga tsohuwar mu ta fito daga dakin barci da ta ji kuwace-kuwace. A kokarin ta na kare Abeeb daga harin Lukma, shikenan sai ya hari maman mu da addan; Yana kokarin sare ta akai ke nan sai ta tara hannun ta, kawai sai Lukman ya gunce mata hannu” inji Azeez, daya daga cikin yaran tsohuwar da Lukman ya gunce wa hannu.

Tsohon Lukman, ko da shike yayi rokon cewa kada a bayyana sunan sa, ya fada da cewa “Hankali na ya tashi kwarai da gaske lokacin da na ga yanayin. “Ina a gidana sai ga kira da cewa Lukman ya aiwatar da wannan mugun abin”

“Na tsorata kwarai da gaske da na isa wajen, na kuma ga yadda yanayin ya kasance”

“Lukman ya kasance a gida na wuni daya kamin abin ya faru. Amma abin mamaki shine, bai nuna wata alaman mutun mai kulle da wata mugun shiri ba” inji babban Lukman a lokacin da yake bayani da manema labarai a nan Asibitin da ake bada kulawa ga malama Muibat.

An bayar da cewa jami’an tsaron shiyar sun kame Lukman, sun kuma sa shi a kulle nan ofishin su.

“Ana kan karin bincike a kan lamarin” inji daya daga cikin jami’an tsaron da ke karar Lukman.