Manyan Labarai daga Jaridun Najeriya ta ranar Talata, 6 ga Watan Agusta, Shekara ta 2019

Wadannan ne Manyan Labarai ta Jaridun Najeriya a yau Talata, 6 ga Watan Agusta, 2019

1. Kotu Ta Bai wa El-Zakzaky Izinin Tafiya kasar Turai don binciken Lafiyar Jiki

Shugaban ‘Kungiyar ci gaban Musulunci ta Najeriya (IMN) da aka fi sani da ‘Yan shi’a, Sheikh Ibrahim El-Zakzaky ya sami izinin tafiya zuwa kasar Turai don kula da lafiyar jikinsa da ta matarsa.

Naija News Hausa ta samu tabbacin hakan ne bisa umarnin da Kotun koli ta jihar Kaduna ta bayar a ranar Litinin, 5 ga watan Agusta a wata hukuncin da Mai shari’a Darius Khobo ya yanke.

2. Kotun Shugaban kasa: Abinda Kotu ta Bayyana ga Jam’iyyar HDP Game da Nasarar Buhari

Kotun daukaka kara ta Shugaban kasa a ranar Litinin da ta gabata, ta tanadi hukunci a cikin karar da Jam’iyyar Hope Democratic Party, HDP ta shigar a gabanta akan kalubalantar nasarar shugaban kasa Muhammadu Buhari a zaben shugaban kasa ta ranar 23 ga watan Fabrairu da ta wuce.

Ka tuna da cewa a baya, Jam’iyyar tare da wasu Jami’o’i sun bayyana rashin amincewa ga matakin Hukumar INEC na sanar da nasarar shugaba Muhammadu Buhari bisa sakamakon da suka gabatar.

3. Hukumar DSS Sun shirya da Sakin El-Zakzaky Da Matarsa

Shugaban ƙungiyar ci gaba da Harkar Musulunci ta Najeriya (IMN), Sheikh Ibrahim El-Zakzaky da matarsa ​​Zeenat za su shaka iskar ‘yanci ba da jinkirta ba, a yayin da hukumar tsaro ta DSS ke shirin tabbatar da sakinsa sa tare da matarsa.

Naija News ta fahimta da cewa wannan ci gaban ya biyo ne bayan da Mai shari’ar Kotun Koli ta jihar Kaduna, Darius Khobo, ya bada umarnin a saki El-Zakzaky da matarsa ​​Zeenat bayan shekaru a katangewar gwamnatin Tarayya a jagorancin shugaba Muhammadu Buhari.

4. Abin da ya zan Dole ga sabbin Ministocin Buhari da yi kafin rantsar da su – CCB

A yayin da ake shirin kadamar da hidimar rantsar da sabbi Ministocin da shugaba Muhammadu Buhari ya gabatar don fara aiki a ofishin su, Hukumar Code of Conduct Bureau (CCB) ta bukace su da su bayyana dukiyar su kamin lokacin rantsar da su ya gabato, ko kuma su shirya da fuskantar doka.

Naija News Hausa ta samu tabbacin hakan ne a wata gabatarwa da Shugaban CCB, Farfesa Muhammed Isah, ya bayar a lokacin da yake bayani game da ministocin.

5. #RevolutionIsNow: Dalilin da yasa muka watsar da Tear Gas ga masu Zanga-zangar – Yan sanda

‘Yan sanda sun ba da hujjar matakin da suka dauka na watsar da mugun hayaki mai sa hawaye da aka fi sani da ‘Tear Gas’ ga wasu masu zanga-zanga da ikirarin #RevolutionNow a birnin Legas

Kamar yadda Naija News da wasu rahotannai suka ruwaito a baya, jami’an tsaro sun ci karo da wasu daga cikin masu zanga-zangar a babban filin wasa da ke a jihar Legas.

6. Kasafin Kuɗaɗen da Gwamnatin Tarayya ta shirya don kashewa ga Ruga a shekarar 2019

Matakin dakatar da tsarin warware Ruga a kasar Najeriya da Shugaba Muhammadu Buhari yayi ya haifar da kwanciyar hankali da zamantakewar al’umma a kasar.

Bisa bincike da la’akari da wahayin da mai taimaka wa Shugaba Buhari, Ita Enang ya bayar, ya bayyana da cewa an ware naira biliyan 2.2b a cikin kasafin kudin 2019 don kafa Ruga.

7. Cin Mutunci Al’Umma – Gani Adams ya kalubalanci DSS a kan kama Sowore

Gani Adams, Aare Onakakanfo na Yarabawa, ya kafa bakin sa ga kiran neman a saki Omoyele Sowore, dan takarar shugaban kasa a zaben 2019 daga Jam’iyyar African Action Congress (AAC).

Ka tuna da cewa Hukumar DSS sun kama Sowore, wanda aka sani da zama shugaban gidan jaridar Sahara Reporters, akan wata Zanga-zanga da ya shirya da yi a dukan kasar.

8. IMN ta mayar da Martani ga matakin Kotu da bayar da damar ‘yanci ga El-Zakzaky da Matar sa

Ka tuna, kamar yada Naija News ta sanar a baya da cewa kotun koli ta jihar Kaduna a jiya Litinin, ta bayar da umarnin a saki Sheikh Ibrahim El-Zakzaky da matarsa ​​Zeenat don su tafi kasar Turai don binciken lafiyar jikinsu.

A cikin hanzari, Kungiyar IMN ta yaba wa umarnin kotun, da fadin cewa lalai wannan matakin ya bayyana nasara ga kudurinsu da kare kai yayin fuskantar zalunci.

Ka sami kari da cikakken Labaran Najeriya a shafin NaijaNewsHausa

Manyan Labarai daga Jaridun Najeriya ta ranar Litini, 5 ga Watan Agusta, Shekara ta 2019

Wadannan ne Manyan Labarai ta Jaridun Najeriya a yau Litini, 5 ga Watan Agusta, 2019

1. A karshe Hukumar DSS ta mayar da martani ga Kama Sowore Tare Da bada dalilan haka

Hukumar Tsaro da Bincike ta Jiha (DSS), a karshe ta mayar da martani da bayyana tabbacin kamun Omoyele Sowore, dan takaran kujerar shugaban kasa ga zaben 2019 da kuma mai wallafa labarai a shahararren gidan labaran yanar gizo mai suna Sahara Reporters.

Hukumar Tsaron a cikin sanarwar da ta bayar, ta bayyana da cewa sun fahimtar cewa zanga-zangar Sowore da barazanar sa zai iya tayar da kwanciyar hankali a kasar.

2. An kashe Shugaban Kungiyar Miyetti Allah a Jihar Adamawa

‘Yan hari da bindiga da ba a san da su ba sun kashe Saidu Kolaku, shugaban kungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria (MACBAN) a jihar Adamawa.

Naija News Hausa ta gane da cewa maharan sun fada ne a gidan Kolaku a ranar Asabar da ta gabata, suka kuma harbe shi har ga mutuwa.

3. Obasanjo Ya gana da Hausawa/Fulani, Kudu maso Yamma tare da Shugabannin Kogi

Tsohon shugaban kasar Najeriya, Olusegun Obasanjo ya gana da shugabannin Hausa/Fulani a yankin kudu maso yamma, Kogi da kuma jihar Kwara.

Naija News ta fahimci cewa taron wanda ya Obasanjo ya wakilta a jihar Abeokuta Ogun ya kasance ne akan rashin tsaro da sace-sacen mutane a yankunan.

4. Masu Zanga-Zangar Juyin Zamantakewa sunyi barazanar ci gaba da Zanga-zangar

Kungiyar Zanga-zanga akan neman juyin mulki da zamantakewa bayyana barazanar ci gaba da zanga-zangar su a ranar Litini ɗin nan duk da cewa hukumar DSS ta kame Sowore, jagoran zanga-zangar.

Naija News ta fahimci cewa shugaban jami’an tsaron Najeriya, IGP Mohammaed Adamu ya gargadi masu zanga-zangar da barazana cewa su janye daga hakan, amma duk a banza.

5. DSS na katange mu daga ganawa da Sowore – Lauya

Shugaban kungiyar lauyoyi ta African Action Congress (AAC), Tope Akinyode, ya bayyana cewa hidimar hukumar DSS na hana kungiyar su da damar ganawa da Omoyele Sowore.

Naija News Hausa ta tuna da cewa an kama Sowore ne a safiyar ranar Asabar da ta gabata a kan zanga-zangar da ya jagoranta da kuma shirin kadamarwa a dukan fadin kasar.

6. Kada ka ba da wata sabuwar sanarwar, Kotu ta gargadi Obaseki

Wata babbar kotun kolin tarayya da ke a Fatakwal a jihar Rivers ta umarci gwamna Godwin Obaseki na jihar Edo da cewa kada ya fitar da wata sabuwar wallafin sanarwar kamar yadda majalisar dattawan Najeriya suka bukace shi da hakan a baya.

Kotun ta ba da wannan umarnin ne bayan bukatar da Mataimakin Shugaban Majalisar Jihar Edo, Hon. Yekini Idiaye ya gabatar a kotun.

7. ‘Yan Sanda sun Kama ‘yan hari da makami da suka kashe Babban Firist na Katolika A Enugu

Rundunar Jami’an tsaron ‘yan sanda ta reshen jihar Enugu sun kama wasu da ake zargi da kisan wani jagoran cocin Katolika da ke a jihar Enugu, Rev Fr Paul Offu.

Naija News ta samu tabbacin hakan ne a wata sanarwa da kwamishinan ‘yan sanda na jihar, Suleiman Balarabe, ya bayar a ganawarsa da manema labarai a Enugu, a ranar Asabar, 3 ga Agusta da ta gabata.

8. Boko Haram Sun kashe Mutane sama da 27,000 Tun daga shekarar 2009 – UN

Bisa wata bayanai da Majalisar Dinkin Duniya ta fitar kwanan nan, sun bayyana da cewa akalla mutane sama da 27,000 ne kungiyar ‘yan ta’adda ta Boko Haram suka kashe tun daga hare-harensu a shekarar 2009 a Najeriya.

Edward Kallon, mai ba da agaji na Majalisar Dinkin Duniya a Najeriya, ya ce a kwanan nan kimanin mutane dubu 130 ne suka fice daga muhallansu, a yayin da masu ‘yan ta’addan suka kuma ci gaba da kafa sabuwar rukuni ISIS a Yammacin Afirka (ISWAP) don fatattakar da Boko Haram.

Ka samu kari da cikakken Labaran Najeriya a shafin NaijaNews.Com

AAC sun dakatar da Ciyaman na Jam’iyyar su, Sowore

Jam’iyyar Siyasa ta African Action Congress (AAC) sun gabatar da dakatar da Omoyele Sowore a matsayin Ciyaman na Tarayyar Jam’iyyar, hade da wasu kuma daga Jam’iyyar.

Naija News ta gane da hakan ne a wata sanarwa da Ciyaman na Kwamitin Jam’iyyar ya bayar a yau Litini, 13 ga watan Mayu, 2019 a birnin Abuja.

Ka tuna da cewa Omoyele Sowore na daya daga cikin ‘yan takaran kujerar shugaban kasan Najeriya daga Jam’iyyar AAC, a zaben shugaban kasa ta shekarar 2019 da aka kamala a baya.

Bisa ganewar wannan gidan labarai tamu, Jam’iyyar sun dakatar ne da Sowore akan laifin kadamar da Makirci, halin cin hanci da rashawa, da kuma rashin bayyana ga wata zama da Jam’iyyar ta yi.

Kwamitin Jam’iyyar (NEC) sun nada Mista Leonard Nzenwa a matsayin sabon ciyaman na Jam’iyyar bayan da aka dakatar da Sowore.

Naija News Hausa ta kuma gane da cewa ba Sowore ne kawai Jam’iyyar suka dakatar ba, amma har da rukunin shugabancin sa a Jam’iyyar.

KARANTA WANNAN KUMA; An Kashe wani Jigon Jam’iyyar APC a Jihar Rivers

Manyan Labarai daga Jaridun Najeriya ta ranar Alhamis 24, ga Watan Janairu, Shekara ta 2019

Wadannan ne Manyan Labarai ta Jaridun Najeriya a yau Alhamis 24 ga Watan Janairu, 2019

 

1. Zan biya ma’aikata kankanin albashi na 100,000 idan aka zaɓe ni – Sowore

Dan takarar shugaban kasa Najeriya na Jam’iyyar (AAC), Mista Omoyele Sowore ya yi alqawari da cewa, idan har aka jefa masa kuri’a kuma ya ci zaben shugaban kasa ta gaba, zai biya ma’aikata 100,000 a matsayin albashi mafi kankanci.

Dan takaran ya yi wannan alkawarin ne a wata ganuwa da suka yi da manema labaran NTA da DARIA a birnin Tarayya, Abuja.

2. Dalilin da ya sa bamu Karawa Shugaba Buhari ba – Bukola Saraki

Majalisar Dinkin Duniya ta dakatar da shirin ta na rinjayar Shugaba Muhammadu Buhari a kan dokar zaɓen da ya ki kadamarwa saboda rashin samun mutanen da daman da suka sanya hannu ga yin hakan, in ji Sanata Bukola Saraki.

Sanatan ya gabatara da wannan ne a ranar Laraba da ta wuce ga manema labaran wata gidan telebijin.

3. ‘Yan sanda sun yi watsi da zargin cewa sun kame Rotimi Amaechi a filin jirgin saman Port Harcourt

Rundunar Jami’an tsaron ‘Yan Sanda da ke a Jihar Rivers sun karyace zancen da ake yi da jam’iyan na cewa sun kama tsohon gwamnan jihar da ministan harkokin sufuri, Mista Rotimi Amaechi.

Ofisan Yada Labarai na Jami’un, (PPRO) Nnamdi Omoni ya yi gabatarwa a yayin da ya wakilci Kwamishanan Jami’an Jihar, Usman Belel da cewa duk fade-faden karya ne da kuma shirin masu makirci.

4. Oby Ezekwesili ta janye daga tseren takarar shugaban kasa ta shekarar 2019

‘Yar takarar shugaban kasa na Jam’iyyar Allied Congress (ACPN), Oby Ezekwesili ta janye daga tseren zaben shugaban kasa da za a  yi a ranar 16 ga Watan  Fabrairu.

Mun sami tabbacin hakan a Naija News da cewar ‘yar takaran ta yi hakan ne yau da safen Alhamis 24 ga watan Janaiiru, da cewa wannan matakin nata tayi shi ne don taimakawa wajen cin nasara ga Jam’iyar APC da Jam’iyyar PDP.

5. Bayanin banza ce na cewar Atiku ya samu shiga Amurka ne a matsayin ma’aikaci na – Saraki

Shugaban Majalisar Dattijan Najeriya, Sanata Bukola Saraki ya ce “dan takarar shugaban kasa na Jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar bai tafi Amurka ba a matsayin mataimaki na”.

A yayin da ya ke bayani da wata gidan talabijin a ranar Laraba, Saraki ya ce “Zancen banza ce da cewa Alhaji Atiku Abubakar ya bi ni zuwa kasar Amurka ne a matsayin mataimaki na”. in ji shi.

6. Nnamdi Kanu ya bayyana yadda Atiku ya bada tabbacin cewa Buhari ‘Jubril’ ne

Shugaban kungiyar Biafra (IPOB), Nnamdi Kanu ya yi zargin cewa Atiku Abubakar, dan takaran shugaban kasa na Jam’iyyar PDP ya bada karin tabbaci na cewar Shugaba Muhammadu Buhari ‘Jubril’ ne da ake batu.

Ya ce, a gabatarwar Atiku a ranar Talata da ta wuce, ya bayyana da cewa lallai Buhari bai jin yaren Fulfude (Fulani). Wannan shi ne tabbacin shi na cewar a musanya shugaba Muhamamdu Buhari da ‘Jubril’.

7. Kotun Koli ta Tarayya ta sake tsarafa Alkalan ta

Matakin tsarafa alƙalai da kotun koli ta birnin tarayyar ta gudanar ya mayar da Alkali Okon Abang zuwa Abuja, Alkalin da daman aka kaishi birnin Asaba shekaru biyu da suka gabata ya dawo Birnin Abuja.

Wannan matakin ya abku ne a yayin da gwamnatin tarayya ke ƙoƙari ta tsige babban Alkalin Shari’ar kasar Najeriya, Walter Onnoghen akan rashin bada kasafin kudi da ya dace kamar yadda doka ta bayar.

8. Sojojin sun ce karya ne da zargin da ake yi, Babu tashin hankali a Jihar Delta

Rundunar sojojin Najeriya sun mayar da martani game da fade-faden da ake yi da cewar akwai tashin hankali a Jihar.

“Wannan karya ce da kulle-kullen makirci daga wasu don tayar da hankalin jama’a.

9. Nine na fara bayanna makircin babban Alkali CJN Onnoghen – in ji Sowore

Dan takarar shugaban kasa na Jam’iyyar (AAC), Omoyele Sowore ya ce shi ne mutumin da ya fara gabatar da makirci da halin rashin gaskiyar Babban Alkalin Shari’ar Najeriya, (CJN) Walter Onnoghen wanda ke da asusun kudi da ba a san da su ba.

Dan takaran ya bayyana wannan ne a ranar Laraba da ta wuce a wata ganawa da abokin takaran sa na Jam’iyyar ACC, Dokta Rabiu Rufai ya halarta.

10. ‘Yan Ta’addan Boko Haram sun kai hari a garin Geidam dake jihar Yobe

‘Yan Boko Haram sun kai farmaki a garin Geidam, ta Jihar Yobe da harbe-harbe ga mazaunan birnin.

A bayanin mazaunan wajen, ‘yan ta’addar sun yi amfani da kasuwa ne don gurfanar da wannan mugun harin.

‘Yan ta’addan sun fado wa garin ne da farmaki misalin karfe 5:30 na maraice a inda suka shigo da harbe-harbe ga iska.

 

Ka sami karin labaran Najeriya a shafin Naija News Hausa