Kalli dalilin da yasa Gwamnatin Jihar Zamfara ta dakatar da Sarakai biyu a ranar guda

Gwamnatin Jihar Zamfara ta dakatar da Sarkin Maru, Alhaji Abubakar CIKA Ibrahim da wakilin kauyan Kanoma, Alhaji Ahmed Lawal da zargin hada hannun da ‘yan ta’adda a Jihar.

Naija News Hausa ta gane da hakan ne bisa wata sanarwa da aka bayar daga hannun Alhaji Yusuf Idris, darakta Janar na sadarwa ga Gwamnan Jihar, a jagorancin sabon gwamnan Jihar, Alhaji Bello Matawalle.

Gwamnatin Jihar ta tsige ‘yan sarauta biyun ne bayan zarge-zarge da alamar da aka gane da su na hada kai da ‘yan hari don aiwatar da mumunar hali a yankin.

A haka kuma aka bukacesu da barin kujerar wakilcin su da kumar mikar da gurbin ga wasu har sai an gama bincike kan zargin.

A fahimta da ganewar Naija News Hausa, bisa rahotannai da tarihi kuma, a karamar hukumar Maru inda aka tsige masu sarauta biyun ne mahara da bindiga suka fara kai hari a kauyan Langido a shekarar 2011 da ta shige a baya.

Ka tuna da cewa a baya kuma, tsohon gwamnan Jiahr, Alhaji Abdul’aziz Yari da tsige ‘yan sarauta shidda a Jihar a lokacin da yake kan jagoranci.

Naija News Hausa ta ruwaito a baya da cewa rundunar Sojojin Najeriya sun harbe mutane biyu a wata farmaki da ya tashi a yayin da tulin mutane ke wata zanga-zanga a shiyar Gurin, a karamar hukumar Fufore ta Jihar Adamawa.

Wannan ya faru ne a yayin da mutanen yankin sun fita zanga-zanga akan rashin amincewa da umarnin hana amfani da babura da jami’an tsaro a goyon bayan gwamnatin jihar ta gabatar da shi.

Gwamnan Zamfara ya bada Naira Miliyan N83m don sayan Shanayan Sallar Eid El-Fitr

Naija News Hausa ta karbi rahoto da tabbacin cewa Gwamnan Jihar Zamfara, Gwamna Bello Matawallen-Maradun ya bada kudi naira Miliyan Tamanin da Takwas (N83,000,000) don sayan shanaye 750 ga hidimar Sallar Eid-El-Fitr a Arewacin kasar Najeriya.

Bisa bayanin Mista Idris Yusuf Gusau, Daraktan Sadarwa ga Jihar ya bayyana cewa shanaye 750 da za a saya din za a rabar da su ne ga ragaggagu, gwamraye, yara marasa iyaye da ke a Jihar, don taimaka masu a wannan lokacin lokacin hidimar Sallah.

Haka kuma Gwamnan, Matawallen-Maradun ya gargadi al’ummar jihar da yin amfani da wannan lokacin azumin Ramadan da kuma hidimar Sallar Eid-El-Fitr da ke gaba don neman fuskar Allah ga kwanciyar hankali, zamantakewa da ci gaba a Jihar.

Mun ruwaito a Naija News Hausa a baya cewa Gwamnan Jihar Zamfara, Bello Matawalle ya sanar da cewa jihar zata fara tsarafa manja a Zamfara.

“Za mu hada hannu tare da abokan kasashen waje don gabatar da itatuwan kwakwa don tsarafa manja a jihar” inji Matawallen-Maradun.

Ya kara da cewa jihar zata sake farfado da aikin noma don inganta shi hakan a Zamfara.

Za a fara Tsarafa Manja a Jihar Zamfara – Matawalle

Gwamnan Jihar Zamfara, Bello Matawalle ya sanar da cewa jihar zata fara tsarafa manja a Zamfara.

Naija News Hausa ta gane rahoton ne bisa bayanin da Matawalle ya shaidawa manema labaru a ranar Alhamis a Gusau cewa gwamnatin jihar za ta zuba jari ta kwarai da gaske ga aikin gona tare da kulawa ta musamman ga tsarafa manja.

Ya ce “Za mu hada hannu tare da abokan kasashen waje don gabatar da itatuwan kwakwa don tsarafa manja a jihar.

Ya kara da cewa jihar zata sake farfado da aikin noma don inganta shi hakan a Zamfara.

“Za mu zuba jarurruka sosai ga hidimar gona a yankunan jihar don taimaka wa al’ummomin karkara don sake dawowa da mummunar asarar da suka sha sakamakon ayyukan da hare-haren ‘yan hari da makami ke kaiwa, da kuma korar su daga gonakin su” inji shi.

“Gwamnatin jihar zata sake farfado da hidimar ban ruwa ga Bakalori don karfafa da kuma yaduwar hatsi a duk shekara a Jihar. zamu kuma kadamar da ayuka da zasu farfado da samar da wutan lantarki a kamfanonin mu” inji  Matawalle.

Mun ruwaito a baya a Naija News Hausa cewa Hatsi na kimanin kudi Miliyan daya (N1m) ta kame da wuta a Jihar Jigawa.

2019: Kotu ta bada Nasarar Zaben Gwamnan Jihar Zamfara ga Dan takaran PDP

A yau Jumma’a, 24 ga Watan Mayu 2019, Kotun Koli ta birnin Abuja ta gabatar da tsige dan takaran kujerar Gwamnan Jihar Zamfara daga Jam’iyyar APC a zaben 2019.

Naija News ta samu sanin cewa Kotun ta yi hakan ne bisa gane da cewa dan takaran na Jam’iyyar APC bai kasance da zaben Firamare ba.

Karar da Alkalan Kotu biyar suka wakilta ya karshe a kan dakatar da dan takaran APC da zargin cewa Jam’iyyar bata kadamar da hidimar zaben Firamare ba a Jihar, kamar yadda aka sanar a shafin labarai a watannan da suka gabata.

Bisa rahoton da aka bayar ga Naija News Hausa a yau, Kotun, a jagorancin Alkali Paul Adamu Galinji, ta gabatar da yin watsi da dukan kuri’un da Jam’iyyar APC ta samu a zaben 2019, an kuma bayyana dan takara na biye da shi ga sakamakon zaben Gwamnoni Jihar a matsayin tabbatacen mai nasara ga zaben.

Alkalin ya kuma gabatar da zargin biyan kudi naira Miliyan Goma N10m ga Jam’iyyar APC.

Kwamitin Kotun ta kuma kalubalanci dukan ‘yan siyasa da janye daga halin raunana dimokradiyyar kasar Najeriya.