Connect with us

Labaran Najeriya

‘Yan Najeriyar Za Su Fuskanci Mawuyacin Yanayi A Karkashin Mulkin Buhari a 2020 – Shehu Sani

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Shehu Sani, tsohon Sanata wanda ya wakilci Kaduna ta Tsakiya a jagorancin Sanatoci na 8 na Najeriya, ya ce ‘yan Najeriya za su kara fuskantar wahala a karkashin Shugaba Muhammadu Buhari a shekarar 2020.

Naija News ta samu labarin cewa tsohon dan majalisar ya yi wannan tsokaci ne yayin wani shirin rediyo a gidan Rediyon Invicta FM a Kaduna ranar Lahadin da ta gabata.

Tsohon Sanata da ya wakilci Kaduna ta tsakiya a majalisar dattijai, Sanata Shehu Sani a ranar Laraba ya yi alfahari da cewa bai janye daga siyasa ba, yana nan dawo nan da shekarar 2023.

Shehu ya bayyana hakan ne a gidansa da ke Kaduna lokacin da kungiyar Magabata na Sabon Garin Nassarawa suka ba shi wata kyautar lambar yabo don kyakyawan aikinsa da kuma halin karimci ga wakilcin al’umma.