Connect with us

Labaran Najeriya

Goodluck Jonathan Ya Bayyana Abin Da Jami’an Tsaro Zasu Yi Kan Wadanda Suka Kai Hari Gidansa

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Ebele Jonathan ya yi kira ga jami’an tsaro da su yi bincike kan harin da wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su waye ba suka kai wa gidansa.

Kamfanin dillancin labarai na Naija News ta ba da rahoton cewa, tsohon shugaban bai sami rauni ba a harin wanda aka yi zargi da kisan gilla ne.

Ko da shike wani jami’in tsaro da ke tsaye a gidan ya lashe mutuwa a harin amma har yanzu ‘yan sanda basu fitar da wata sanarwa ba.

Naija News ta ruwaito da cewa Jonathan Jonathan ya yi kira ga hukumomin tsaro a karkashin jagorancin shugaba Muhammadu Buhari da su kama wadanda suka aiwatar da wannan harin da kuma tabbatar da cewa irin wannan harin kunar bakin wake bai sake faruwa ba a cikin harabarsa ko wani wuri a cikin kasar ba.

Tsohon shugaban ya bayyana harin da wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba suka kai masa a gidansa da “marasa tausayi”.

“Ku yi taka-tsantsan yayin da kuke kokarin kame da hukunta wadanda suka aikata wannan mumunar harin da kuma tabbatar da cewa wannan mummunan harin bai sake faruwa a kowane bangare na kasar nan.” Inji Jonathan.