Connect with us

Labaran Najeriya

Buhari Da Bakare Sunyi Wani Ganawar Siiri A Aso Rock

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Fasto Tunde Bakare, babban Fasto na Majami’ar Latter Rain a ranar Litinin, ya yi wata ganawar siiri da Shugaba Muhammadu Buhari a fadar shugaban kasa a Aso Rock Villa, Abuja.

Ganawar siiri da Bakare yayi tare da Shugaban kasar ta fara ne da misalin karfe 3 na rana, kuma ya dauki kusan mintuna 30 kamin karsheta.

Ku tuna Naija News Hausa ta ruwaito a baya da cewa Babban Fasto da Jagoran Ikilisiyar ‘The Latter Rain Assembly’ a jihar Legas, Fasto Tunde Bakare ya baiyana da cewa shi ne zai zama Shugaban kasar Najeriya a shekarar 2023.

Babban Malami da Faston ya baiyana da cewa zai karbi mulki daga hannun Shugaba Muhammadu Buhari lokacin da wa’adinsa ya kare a shekarar 2023.

A cikin baiyanin sa ya ce; “Shugaba Muhammadu Buhari ne na Goma shabiyar ga Mulki, nine kuwa na Goma sha shidda.”