Connect with us

Labaran Najeriya

DSS Sun Kame Wanda Ya Shirya Bidiyon Shairi Kan Auren Shugaba Buhari Da Zainab, da Sadiya Farouq

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Ofishin Hukumar Tsaron Kasa (DSS) at sanar da kama Kabiru Mohammed, mutumin da ake zargi da kulla shellan karya kan auren Shugaba Buhari.

Naija News ta tuna cewa an bayyana wani rahoto a kusan  Oktoba ta shekarar 2019 cewa Shugaba Buhari ya shirya aure da Ministan Kulla da Al’umma, Sadiya Umar Farouq.

Day Dr. Peter Afunaya, kakakin yada yawun hukumar ke bada bayani kan lamarin, ya ce, an fara gudanar da bincike ne, biyo bayan korafin da Ministan Kudi ya yi wa Ma’aikatar.

Naija News ta fahimci cewa an kama Mutumin, mai shekaru 32 ga haifuwa ne saboda kirkirar wata bidiyo da kuma yada bidiyon karyar wanda ke nuna Shugaba Muhammadu Buhari na bikin auren Ministan Kasa, Zainab Ahmed da Ministan Harkokin Al’adu da Ci gaban Jama’a, Sadiya Farouq.

Ya bayyana da cewa sunyi kamun ne bayan da daga cikin Ministocin tayi gabatar da karar a ofishin su da neman su kame duk wanda suka gane da shirya da kuma watsar da bidiyon.

“Hukumar mu kuwa ta gane da kuma kame wanda ya shirya da kuma watsar da bidiyon. Sunansa Kabiru Mohammed. Dan Kano ne da kuma shekara ga 32 haifuwa. Ya kuma karanci yaran Fulfude da Hauda a makarantar jami’a ta Federal College of Education, Kano, da kuma karatun sashin Sadarwa daga Aminu Kano Islamic School.“

“Ya riga ya amince da aikata hakan kuma mun ci gaba da bincike kan dalilin hakan.” Inji shi.

Mutumin kuwa a ganewar Naija News Hausa ya nemi afuwa kan laifin sa da kuma bayyana cewa lallai aikin Sheidan ne. Ya kuma kara da cewa shi dan Jam’iyyar

Kwakwasiya ne a jihar Kano.