2023: Kalli Yankin Da Matasan Arewa Suka Ba wa Goyon baya Ga Shugaban Kasa

Wata gamayyar kungiyoyin matasan Arewa ta yi kiran da a sauya shugabancin kasar daga arewa zuwa yankin Kudu maso Kudu kafin zaben shugaban kasa a shekarar 2023.

Hadin gwiwar, a karkashin kungiyar ‘Arewa Youths Assembly’, ta ce ba zai zama da adalci ba ga Arewa ta fito da shugaban Najeriya na gaba tare da lura cewa yankin ta mamaye matsayin fiye da sauran yankuna tun bayan da kasar ta samu ‘yancin kanta a 1960.

Saboda haka, kungiyar sun bayyana cewa sun fara neman dan takara daga Kudu maso Kudu mai shekarun haifuwa tsakanin shekara 40 zuwa 50 da zai karbi shugabanci daga Shugaba Muhammadu Buhari a 2023.

Shugaban kungiyar, Mohammed Salihu Danlam ne ya bayyana wannan matsayin kungiyar a gaban wani taron manema labarai a jiya.

Yayin da Danlam ke jawabinsa, ya bayyana cewa dan takarar “dole ne ya kasance yana da cudanya na kwarai da kasashen duniya, dole ne ya shiga cikin tsarin mulki na lokaci mai tsawo, ya kasance da kwarewar sadarwa, dole ne ya zama iya ba da fifikon tabbatar da adalci na zamantakewa da kyautatawa kan ci gaban tattalin arziki.”

“Arewa ta mamaye matsayin shugabancin kasar nan tun lokacin da ta sami ‘yancin kai, fiye da kowane yanki; lokaci ya yi da matasan Kudu maso Kudu za su fitar da shugaban kasa shekarar 2023,” in ji Danlam.

“Najeriya kasa ce da ke baya a tsakar cin gaba da alkawurai da kuma zama cikin duhun rashin adalci. Muna rayuwa da rashin tabbas. A yadda abubuwa suke a yanzu, bamu da masaniyar al’ummar da za su faru idan Arewa ta ci gaba da mulki a 2023. inji shugaban Kungiyar Matasan Arewa.