Kannywood: Takaitaccen Labarin Jaruma Jamila Nagugu

A yau Naija News Hausa ta na gabatar maku da takaitaccen Sarauniyar Kannywood, da aka fi sani da Jamila Nagudu, a yadda sunan nata yake.

Ka tuna a baya Naija News ta ruwaito da cewa Jamila Nagugu ta ce ‘Ba Ta son ta Auri Mai Arziki.

A takaice dai, Jaruma Jamila Nagudu ‘yar wasan finafinan Hausa ce wacce aka Haifeta a ranar 10 ga watan Agusta.

Jamila Umar Nagudu a nata bangaren Sarauniyar Kannywood ce, ma’ana, ita babbar jaruma mace ne a fagen shirya fina-finan Hausa, watau Kannywod wacce take da hedkwatarta a Kano, arewacin Najeriya.

Jarumar ta shiga fagen masana’antar fim na Hausa ne shekaru da yawa baya, amma ‘yan shekaru da suka gabata, babban Froduza na fina-finai, Aminu Saira ya sanyata a cikin fitaccen fim din da aka yi wa take ‘Jamila da Jamilu’, watau tun a fim dinne tauraron jaruma Jamila ya haska da bayyana ta ko ta ina saboda irin kwarewa da taka rawar gani a fim din.

Jamila dai ta sami lambobin yabo bakwai na masana’antu kuma ta fice a fina-finai da yawa.

A wata ganawa da Jaruma Jamila tayi da BBC Hausa a shekarar 2016, Nagudu ta shaida wa BBC cewa ba ta da saurayi a cikin masu yin fina-finai a Kannywood.

Amma dai a lokacin hirar ta kara da cewa idan ta gamu da wanda ranta ke so a cikin abokan aikinta ba za ta yi kasa-a-gwiwa wajen aurensa ba.

A cikin karin bayanin nata, Fitacciyar jarumar ta yi watsi da zarge-zargen da ake yi wa ‘yan fim cewa ba sa son yin aure, tana mai cewa “idan lokacin yin auren mutum bai yi ba babu yadda za a yi ya yi da kansa”.

“Mutanen da suke cewa ba ma son zaman aure, su dubi sauran al’umma mana. Akwai mata da yawa wadanda suka girme ni amma ba su da aure saboda Allah bai sa lokacin yinsu ya yi ba.” Inji cewarta.

Ga Fina-Finai da dama da Jamila Nagugu ta fice a cikinsu;

Jamila Mai Wasa Da Kura, Kama Da Wane, Kanin Miji, Kishiya Ta, ‘Ya ‘Ya Na, Alhaki Kwikwiyo, Aska Tara, Bashin Gaba, Cikar Burina, Farin Dare, Fataken Dare, Fitilar Dare, Ga Fili Mai Doki, Gamdakatar, Halisa, Haske, Hindu, An African Extra Vagrant, Inda Ranka (Kasha Kallo), Jamila da Jamilu, Jani Jani, Jarumta, Laifin Dadi, Larai, Mai Dalilin Aure (Match Maker), Marayan Zaki, Masu Aji, Muradi, Sai a Lahira, Salma Hayat,
Ya Salam. Da dai sauransu.

DSS Sun Kame Wanda Ya Shirya Bidiyon Shairi Kan Auren Shugaba Buhari Da Zainab, da Sadiya Farouq

Ofishin Hukumar Tsaron Kasa (DSS) at sanar da kama Kabiru Mohammed, mutumin da ake zargi da kulla shellan karya kan auren Shugaba Buhari.

Naija News ta tuna cewa an bayyana wani rahoto a kusan  Oktoba ta shekarar 2019 cewa Shugaba Buhari ya shirya aure da Ministan Kulla da Al’umma, Sadiya Umar Farouq.

Day Dr. Peter Afunaya, kakakin yada yawun hukumar ke bada bayani kan lamarin, ya ce, an fara gudanar da bincike ne, biyo bayan korafin da Ministan Kudi ya yi wa Ma’aikatar.

Naija News ta fahimci cewa an kama Mutumin, mai shekaru 32 ga haifuwa ne saboda kirkirar wata bidiyo da kuma yada bidiyon karyar wanda ke nuna Shugaba Muhammadu Buhari na bikin auren Ministan Kasa, Zainab Ahmed da Ministan Harkokin Al’adu da Ci gaban Jama’a, Sadiya Farouq.

Ya bayyana da cewa sunyi kamun ne bayan da daga cikin Ministocin tayi gabatar da karar a ofishin su da neman su kame duk wanda suka gane da shirya da kuma watsar da bidiyon.

“Hukumar mu kuwa ta gane da kuma kame wanda ya shirya da kuma watsar da bidiyon. Sunansa Kabiru Mohammed. Dan Kano ne da kuma shekara ga 32 haifuwa. Ya kuma karanci yaran Fulfude da Hauda a makarantar jami’a ta Federal College of Education, Kano, da kuma karatun sashin Sadarwa daga Aminu Kano Islamic School.“

“Ya riga ya amince da aikata hakan kuma mun ci gaba da bincike kan dalilin hakan.” Inji shi.

Mutumin kuwa a ganewar Naija News Hausa ya nemi afuwa kan laifin sa da kuma bayyana cewa lallai aikin Sheidan ne. Ya kuma kara da cewa shi dan Jam’iyyar

Kwakwasiya ne a jihar Kano.

2023: Kalli Yankin Da Matasan Arewa Suka Ba wa Goyon baya Ga Shugaban Kasa

Wata gamayyar kungiyoyin matasan Arewa ta yi kiran da a sauya shugabancin kasar daga arewa zuwa yankin Kudu maso Kudu kafin zaben shugaban kasa a shekarar 2023.

Hadin gwiwar, a karkashin kungiyar ‘Arewa Youths Assembly’, ta ce ba zai zama da adalci ba ga Arewa ta fito da shugaban Najeriya na gaba tare da lura cewa yankin ta mamaye matsayin fiye da sauran yankuna tun bayan da kasar ta samu ‘yancin kanta a 1960.

Saboda haka, kungiyar sun bayyana cewa sun fara neman dan takara daga Kudu maso Kudu mai shekarun haifuwa tsakanin shekara 40 zuwa 50 da zai karbi shugabanci daga Shugaba Muhammadu Buhari a 2023.

Shugaban kungiyar, Mohammed Salihu Danlam ne ya bayyana wannan matsayin kungiyar a gaban wani taron manema labarai a jiya.

Yayin da Danlam ke jawabinsa, ya bayyana cewa dan takarar “dole ne ya kasance yana da cudanya na kwarai da kasashen duniya, dole ne ya shiga cikin tsarin mulki na lokaci mai tsawo, ya kasance da kwarewar sadarwa, dole ne ya zama iya ba da fifikon tabbatar da adalci na zamantakewa da kyautatawa kan ci gaban tattalin arziki.”

“Arewa ta mamaye matsayin shugabancin kasar nan tun lokacin da ta sami ‘yancin kai, fiye da kowane yanki; lokaci ya yi da matasan Kudu maso Kudu za su fitar da shugaban kasa shekarar 2023,” in ji Danlam.

“Najeriya kasa ce da ke baya a tsakar cin gaba da alkawurai da kuma zama cikin duhun rashin adalci. Muna rayuwa da rashin tabbas. A yadda abubuwa suke a yanzu, bamu da masaniyar al’ummar da za su faru idan Arewa ta ci gaba da mulki a 2023. inji shugaban Kungiyar Matasan Arewa.

 

Gombe: Dankwambo Ya Caji Membobin PDP Da Su ci Gaba da kasancewa Da Hadin Kai

Tsohon gwamnan jihar Gombe, Ibrahim Dankwambo ya tuhumi membobi na jam’iyyar Peoples Democratic Party a jihar Gombe da su kasance da hadin kai.

Tsohon gwamnan jihar ya bayyana hakan ne yayin da yake jawabi a taron PDP a Gombe ranar Litinin din nan da ta gabata.

Dankwambo wanda tsohon mataimakinsa, Charles Iliya ya wakilta a jawabin, ya bayyana da cewa ayyukan raya kasa a jihar duk a karkashin gwamnatin PDP ne.

Shugaban jam’iyyar PDP a jihar Gombe, Nuhu Poloma, yayin da yake nasa jawabi ya bayyana cewa an kayar da PDP a lokacin babban zaben shekarar 2019 ne saboda sun ki sakacci da yawa.

Poloma ya kara da cewa har yanzu jam’iyyar na da karfi sosai a jihar, duk da kayen da aka yi masu a babban zaben.

Shugaban PDP din ya gargadi mambobin jam’iyyar da bayar da tikitin neman zabe ga daidaikun mutane da suka ci gaba da kasancewa a cikin jam’iyyar koda aka kashe su a jam’iyyar.

Shi kuma Shugaban Jam’iyyar PDP a Bauchi, Hamza Akunya, yayin da yake magana ya ce jam’iyyar ta sha kaye a babban zaben saboda ayyukan wasu membobin jam’iyyar da wasu jam’iyyu.

Akunya ya lura cewa, mambobin jam’iyyar PDP da suka fice daga jam’iyyar nan ba da jimawa ba zasu dawo.

“Shawarata a gare ku ita ce ku samar da sahihan ‘yan takara ga zaben 2023 wadanda zasu iya kayar da ‘yan adawa daga wasu jam’iyyu,” in ji shi.

Wata tsohuwar ‘yar majalisar wakilai, Binta Bello, yayin da take magana ta bayyana cewa an gudanar da taron ne domin hadin kan mambobin jam’iyyar.

Bello wadda itace ta shirya taron ta kara da cewa dole ne membobin jam’iyyar su fahimci cewa har yanzu jam’iyyar tana da karfi a jihar Gombe kuma a shirye take ta taka rawar gani

Gwamna Ganduje Ya Nada Mata Mataimaka na Musamman Guda 5 A Kano

Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Ganduje ya gabatar da nadin wasu mata Biyar a Kano

Wata tsohuwar Kwamishina mai kula da harkokin mata, Hajiya Hajiya Yardada Maikano Bichi, tana daga cikin mata biyar na Musamman Mataimaka, wadanda gwamnan jihar Kano, Dokta Abdullahi Umar Ganduje ya nada.

Gwamna Ganduje bayan nadin dukkansu da kuma bayar da umarnin su fara aiki nan take, ya umarci dukkan wadanda aka nada da su tabbatar da kwarewarsu yayin aiwatar da ayukansu a kowane ofishi.

A cewarsa, “tunda aka zabe ku a cikin jerin mutane da yawa, ya nuna a fili da cewa muna tabbatar wa jihar da cewa kuna da abin da zai kawo ci gaban jihar.”

“Ya kamata ku tabbatar da cewa kun bi dukkanin manufofin gwamnati da shirye-shiryen da suka danganci ofisoshinku, har ma da hakan, kuna kulawa da su da dukkan hankali.”

Wadanda aka nada sun hada da, Hajiya Fatima Abdullahi Dala, a matsayin mai ba da shawara ta musamman a shafin Kulawa ga Yara da kuma Ayukan Mata; Dokta Fauziyya Buba a matsayin mai ba da shawara ta musamman a Ma’aikatar Kiwon Lafiya; Hajiya Aishatu Jaafaru, mai ba da shawara ta musamman kan Shirin ciyar da ‘yan makaranta;  Hajiya Hama Ali Aware kuma a matsayin Mai Bada shawara na musamman akan Zuba Jarin Kasashen waje, da kuma Hajiya Yardada Maikano Bichi, a matsayin Mashawarci na Musamman kan Kungiyoyi masu zaman kansu.

‘Yan Hisbah Sun Kame Wani Dan Sanda Da Wasu Mata Uku a Gusau

Hukumar Hisba ta jihar Zamfara ta bayyana kame wani jami’in ‘yan sanda da wasu mata uku da ake zarginsu da aikata muggan laifuka a wani otal da ke Gusau.

Shugaban hukumar, Dakta Atiku Zawuyya ne ya bayyana hakan yayin da yake gabatar da wadanda ake zargin a hedikwatar hukumar ranar Litinin din nan da ta wuce.

Dakta Zawuyya ya bayyana da cewa an kama jami’in ‘yan sanda da ke aiki tare da ofishin‘ yan sanda ta Central Police Station da ke a Gusau tare da ’yan matan uku a wani ‘Otal, da zargin su da aikata laifin da suka saba wa ka’idar Sharia.

Zawuyya ya ce binciken farko da hukumar ta gudanar ya nuna cewa daya daga cikin ‘yan matan uku da aka kama ta fito ne daga jihar Kaduna yayin da sauran biyun kuma ‘yan gida guda ne a Zamfara.

Shugaban ya ce hukumar sau da yawa ta gargadi masu kula da otal din kan amince da shigar da irin wadannan mutane a Otal din amma sun kasa bin ka’idoji da ke jagorantar gudanar da kasuwancin otal a jihar.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) sun bayar da rahoton cewa, jami’an hukumar Hisba sun kame harda Manaja da ke kula da Otal din.

Zawuyya ya karshe da cewa za a gurfanar da wadanda ake zargin zuwa kotu bayan cikakken bincike. (NAN).

‘Yan Najeriyar Za Su Fuskanci Mawuyacin Yanayi A Karkashin Mulkin Buhari a 2020 – Shehu Sani

Shehu Sani, tsohon Sanata wanda ya wakilci Kaduna ta Tsakiya a jagorancin Sanatoci na 8 na Najeriya, ya ce ‘yan Najeriya za su kara fuskantar wahala a karkashin Shugaba Muhammadu Buhari a shekarar 2020.

Naija News ta samu labarin cewa tsohon dan majalisar ya yi wannan tsokaci ne yayin wani shirin rediyo a gidan Rediyon Invicta FM a Kaduna ranar Lahadin da ta gabata.

Tsohon Sanata da ya wakilci Kaduna ta tsakiya a majalisar dattijai, Sanata Shehu Sani a ranar Laraba ya yi alfahari da cewa bai janye daga siyasa ba, yana nan dawo nan da shekarar 2023.

Shehu ya bayyana hakan ne a gidansa da ke Kaduna lokacin da kungiyar Magabata na Sabon Garin Nassarawa suka ba shi wata kyautar lambar yabo don kyakyawan aikinsa da kuma halin karimci ga wakilcin al’umma.

Goodluck Jonathan Ya Bayyana Abin Da Jami’an Tsaro Zasu Yi Kan Wadanda Suka Kai Hari Gidansa

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Ebele Jonathan ya yi kira ga jami’an tsaro da su yi bincike kan harin da wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su waye ba suka kai wa gidansa.

Kamfanin dillancin labarai na Naija News ta ba da rahoton cewa, tsohon shugaban bai sami rauni ba a harin wanda aka yi zargi da kisan gilla ne.

Ko da shike wani jami’in tsaro da ke tsaye a gidan ya lashe mutuwa a harin amma har yanzu ‘yan sanda basu fitar da wata sanarwa ba.

Naija News ta ruwaito da cewa Jonathan Jonathan ya yi kira ga hukumomin tsaro a karkashin jagorancin shugaba Muhammadu Buhari da su kama wadanda suka aiwatar da wannan harin da kuma tabbatar da cewa irin wannan harin kunar bakin wake bai sake faruwa ba a cikin harabarsa ko wani wuri a cikin kasar ba.

Tsohon shugaban ya bayyana harin da wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba suka kai masa a gidansa da “marasa tausayi”.

“Ku yi taka-tsantsan yayin da kuke kokarin kame da hukunta wadanda suka aikata wannan mumunar harin da kuma tabbatar da cewa wannan mummunan harin bai sake faruwa a kowane bangare na kasar nan.” Inji Jonathan.

Buhari Da Bakare Sunyi Wani Ganawar Siiri A Aso Rock

Fasto Tunde Bakare, babban Fasto na Majami’ar Latter Rain a ranar Litinin, ya yi wata ganawar siiri da Shugaba Muhammadu Buhari a fadar shugaban kasa a Aso Rock Villa, Abuja.

Ganawar siiri da Bakare yayi tare da Shugaban kasar ta fara ne da misalin karfe 3 na rana, kuma ya dauki kusan mintuna 30 kamin karsheta.

Ku tuna Naija News Hausa ta ruwaito a baya da cewa Babban Fasto da Jagoran Ikilisiyar ‘The Latter Rain Assembly’ a jihar Legas, Fasto Tunde Bakare ya baiyana da cewa shi ne zai zama Shugaban kasar Najeriya a shekarar 2023.

Babban Malami da Faston ya baiyana da cewa zai karbi mulki daga hannun Shugaba Muhammadu Buhari lokacin da wa’adinsa ya kare a shekarar 2023.

A cikin baiyanin sa ya ce; “Shugaba Muhammadu Buhari ne na Goma shabiyar ga Mulki, nine kuwa na Goma sha shidda.”

Manyan Labarai daga Jaridun Najeriya ta ranar Talata, 31 ga Watan Disamba, Shekara ta 2019

Wadannan ne Manyan Labarai ta Jaridun Najeriya a yau Talata, 31 ga Watan Disamba, 2019

1. Shugaba Buhari ya Tsauta Wa Ministoci Da Mataimakansu da Tafiye-tafiye

Shugaba Muhammadu Buhari ya gabatar da wasu sabbin umarni da ke takaita adadin lokuta da Ministoci zasu iya tafiya a cikin shekara guda.

Ministan yada labarai, al’adu da yawon shakatawa, Lai Mohammed ne ya sanar da hakan a ranar Litinin.

2. Buhari Da Bakare Sunyi Wani Ganawar Siiri A Aso Rock

Fasto Tunde Bakare, babban Fasto na Majami’ar Latter Rain a ranar Litinin, ya yi wata ganawar siiri da Shugaba Muhammadu Buhari a fadar shugaban kasa a Aso Rock Villa, Abuja.

Ganawar siiri da Bakare yayi tare da Shugaban kasar ta fara ne da misalin karfe 3 na rana, kuma ya dauki kusan mintuna 30 kamin karsheta a fahimtar Naija News.

3. Buratai Ya Kaurace Wa Taron Da Buhari Yayi Da Shugabannin Ma’aikata

Shugaban kasa Muhammadu Buhari a ranar Litinin din da ta gabata ya yi wata ganawar siiri da shuwagabannin ma’aikata a gidan gwamnati da ke Abuja, an yi imanin cewa taron itace na karshe ga shekara ta 2019.

An yi imanin cewa taron ya kasance ne kan zancen tsaron kasa daga hannun shugabannin tsaro.

4. Buba Galadima Ya Bayyana Wanda Shugaba Buhari yake Tsoro Fiye Da Allah

Buba Galadima, wanda shine tsohon kakakin kungiyar yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar PDP, ya bayyana cewa shugaban kasa Muhammadu Buhari yana tsoron ‘yan farar fata, musamman gwamnatin Amurka fiye da Allah.

Naija News ta ruwaito cewa Galadima yayi wannan furucin ne yayin martani kan ikirarin da Lauyan Janar din kuma Ministan Shari’a, Abubakar Malami, ya bayar cewa an saki Sambo Dasuki, tsohon mai ba da shawara kan harkar tsaro, da Omoyele Sowore, dan jaridar Sahara Reporters, bisa dalilan jin kai.

5. 2023: Buba Galadima ya aika da Gargadi mai karfi ga Tinubu game da Buhari

Alhaji Buba Galadima, jigo a jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) da kuma tsohon abokin hamayya na Shugaba Muhammadu Buhari, ya koka da cewa shugaban kasar ba ya taba taimaka wa kowa.

A cikin bayanin Galadima, ya kara da cewa ba a san Buhari da taba taimakawa wadanda suka taimaka masa a harkan siyasa ba.

6. Gwamnatin Legas Tayi Ikirarin Kame Duk Asibitocin Da Suka gaza bada Kulawa ga wadanda suka jikkata da harbin bindiga

Gwamnatin jihar Legas ta yi kira ga dukkanin asibitoci da wadanda ke a fannin kiwon lafiya, hadi da wadanda ke cibiyoyin kiwon lafiya na gwamnati da na masu zaman kansu da ke aiki a jihar da su daina yin watsi da wadanda ‘yan bindiga suka rutsa da su.

Gwamnatin jihar ta kuma nemi asibitocin da su janye daga halin guji da rashin bada kulawa ga masu mugun rauni a kan uzurin neman rahoton ‘yan sanda ko kuma bukatar samar da shaidar kudade kafin fara jinyarsu.

7. 2020: ‘Yan Najeriyar Za Su Fuskanci Mawuyacin Yanayi A Karkashin Mulkin Buhari – Shehu

Shehu Sani, tsohon Sanata wanda ya wakilci Kaduna ta Tsakiya a jagorancin Sanatoci na 8 na Najeriya, ya ce ‘yan Najeriya za su kara fuskantar wahala a karkashin Shugaba Muhammadu Buhari a shekarar 2020.

Naija News ta samu labarin cewa tsohon dan majalisar ya yi wannan tsokaci ne yayin wani shirin rediyo a gidan Rediyon Invicta FM a Kaduna ranar Lahadin da ta gabata.

8. PDP Ta Kalubalanci APC Akan Yawan Karuwar Rashin Aiki A Najeriya

Jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) ta sake yin tir da jam’iyyar All Progressives Congress (APC) kan karuwar rashin aikin yi a kasar.

A wata sanarwa dauke da sa hannun jami’in hulda da jama’a na jam’iyyar PDP, Mista Kola Ologbondiyan, ya fada da cewa jam’iyyar APC cewa ta lallatar da harkokin kasar ta hanyar tafiyar da harkokin a siyasance da musanman kan yanayin rashin aiki a kasar, da kuma cewa su shirya don fuskantar kalubalan ayukansu a shekara ta 2023.

Ku sami kari da Cikakken Labaran Najeriya ta yau a shafin Naija News Hausa