Connect with us

Labaran Najeriya

Kalli Bidiyon Obasanjo yadda ya bar Najeriya a gurguje bayan nasarar Buhari

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Kalli wata bidiyo da ta mamaye layin yanar gizo
Bidiyon na dauke da yadda tsohon shugaban kasan Najeriya, Olusegun Obasanjo, inda aka nuna shi a gurguje da kokarin barin kasar bayan nasarar shugaba Muhammadu Buhari a zaben tseren kujerar shugaban kasa ta shekarar 2019.

Naija News ta gano wannan bidiyon ne a yayin da ‘yan Jam’iyyar APC da ke kasar Turai suka aika a layin twitter.
Kalli bidiyon a kasa;

Ka tuna a baya tsohon shugaban ya karyace zancen cewa ya gudu zuwa kasar turai bayan nasarar Buhari.

Obasanjo a bayanin sa da manema labarai a gidan sa da ke Abeokuta, Jihar Ogun da cewa karya ne jita-jitan da ya mamaye ko ta ina da cewa ya gudu zuwa kasar waje.

“Me zai sa in gudu daga kasar” inji Obasanjo a bayanin sa da manema labaran.

“Ko ba don komai ba, Daidai ne in tsaya in jefa kuri’a a matsayi na na dan kasar Najeriya ga zaben shugaban kasa da kuma ta gwamnoni da za a yi a watan Maris”

“Duk masu daukar wannan jita-jita ta karyan cewa na guje daga kasar; na bar su da Allah”