Connect with us

Uncategorized

‘Yan Hari da Bindiga sun Sace Insfekta na ‘Yan Sanda, tare da Wasu A Abuja

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

An samu rahoton cewa an sace Insfekta Janar na ‘yan sandan Najeriya (NPF) da wani mutum guda, a kauyen Rubochi da ke Kuje, karamar hukuma a Birnin Tarayyar Najeriya (FCT), Abuja.

Rahoton da aka bayar akan jaridar The Nation wanda jaridar ta Naija News ta gane da ita ya bayyana da cewa an sace Sufeto Janar na ‘Yan Sandar ne da wani mutum a tsakar dare ranar Lahadi, 27 ga Oktoba ta hannun wasu ‘yan hari da bindiga wadanda suka afka wa al’ummar yankin da harbe-harbe.

Naija News Hausa fahimta da cewa masu sace mutanen su sace har da Kani ga tsohon Shugaban Karamar Hukumar Kuje, wanda aka fi sani da Mohammed Galadima, ‘yan kwanaki kadan da suka gabata a cikin wannan yankin.

A wata majiya, an sanar da cewa lamarin ya faru ne da misalin karfe 2 na safiyar ranar Juma’a, yayin da ‘yan bindigar suka fada wa gidan Galadima ta hanyar tsallake shingen gidan, inda kuma suka sace mutumin a gidansa.

Wannan gidan labaran tamu ta gane da cewa ‘yan garkuwan sun bukaci biyan naira Miliyan 10 kamin su sakeshi.

Mataimakin Kakakin yada yawun Rundunar ‘yan sandan Birnin Tarayyar Najeriya (FCT), ASP Mariam Yusuf, a lokacin da aka kira ta da bayani ta bayyana da cewa zata mayar da kira idan ta samu cikakken bayani game da yanayin.