Connect with us

Uncategorized

2016NPOWER: Dalilin Jinkiri Da Biyan Albashin N-POWER Na Watan Aktoba da Nuwamba

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Ministan ba da agaji, kula da bala’i da ci gaban al’umma, Sadiya Umar Farouq ta bayar da bayani kan dalilin da ya sa har yanzu ba a sami biyan albashin watan Aktoba da Nuwamba ga masu aikin N-Power ba.

A cikin bayanin da ta gabatar, har yanzu ba a biya albashi din ba saboda wadanda suka yi rajista a shekarar 2016 ba su fice daga hidimar N-Power din ba.

Mallam Sadiya ta fadi hakan ne a ranar Litinin yayin da take zantawa da manema labarai a birnin tarayyar kasa, Abuja.

Ta ce yakamata a ce wadannan masu amfana da hidimar N-Power tun karo na farko sun kai ga karshe wa da kuma isa ga manyan kamfanoni don karin inganci.

“Na samu rubutattun bayanan farko daga shugabannin hukumomin da shirye-shiryen gabatarwa daga ma’aikatar tun watan Oktoba na 2019. Duk akan gwagwarmaya da wahala da akwai cikin tafiyar da hidimar, a yayin da mika ragamar ke kan gudana” inji Sadiya.

“Game da korafe-korafe da kokawa da ba su dace ba game da rashin biyan albashi na watan Oktoba da Nuwamba na 2019 ga masu cin damar aikin N-Power, ma’aikatar na son ta sake jaddada kudirinta na tabbatar da cewa masu cin damar shirin SIPs din sun samu zarafi mai dacewa akan ƙa’idodin aikin.” 

“Wadanda ke cin damar hidimar N-Power da suka yi rajista a shekara ta 2016 har yanzu ba a fice ba daga shirin, harma watanni 16 bayan karshe kwantiraginsu. Ya kamata su kammala hidimarsu don samun kyakkyawan inganci a gaba.”

“A yanzu haka ma’aikatar tana kokarin kirkirar dabarun ficewarsu, wacce babu shirin haka tun a farko.”

Kodashike, Naija News a baya ta ruwaito da cewa Maryam Uwais, mai ba da shawara ta musamman ga shugaban kasa kan harkar saka jari ta ce an riga an sanya shirye-shiryen ficewa ga masu cin damar aikin N-Power wadanda lokacin hidimar tasu ya kare ko.

Malama Maryam ta fadi hakan ne yayin da take zantawa da manema labaran NAN a ranar Litinin.