Connect with us

Uncategorized

CJN Tanko Muhammad Na Neman Sauya Kundin Tsarin Mulki Don Kafa Sharia A Najeriya

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Babban alkalin Najeriya (CJN), Mai shari’a Ibrahim Tanko Muhammad, ya yi kira da a yi wa kundin tsarin mulkin Najeriya garambawul don ba da dama ga musulmai ga sanya dokar Shari’a a kudin dokar kasa.

Muhammad ya yi wannan magana ne yayin da yake ayyana Taron Majalisar Alkalai na karo 20 wanda aka bude a Jami’ar Ahmadu Bello (ABU), Zariya a ranar Laraba.

Naija News ta fahimci cewa Alkali Muhammad Danjuma, Grand Khadi na jihar Neja ne ya wakilci Babban Alkalin katsar a wajen taron.

Ya ce: “Kamar yadda dukkanmu muka sani, akwai wasu sassan kundin tsarin mulki wadanda suka ba da damar aiwatar da shari’ar dayantaka, kuma ban da wannan, ba za mu iya karin wani abu ba. Muna da lambar da za mu iya gyara kundin tsarkin mulkin don tabbatar da matsayinmu na Musulmai.”

Da yake karin haske a gabatarwan, ya ba da shawarar a koyar da Shari’ar a harshen Larabci a cikin jami’o’in Najeriya kuma ba da yaren Ingilishi ba kamar yadda a halin yanzu yake.

Don haka, ya yi kira ga masana ilimi su yi la’akari da batun saboda la’akari da mahimmancin tsarin shari’ar zuwa ga harkar shari’a.

“Ya kamata ne a dinga koyar da dokar Shari’a da Larabci ba Turanci ba. Babu wata jami’a a Najeriya da ke gudanar da Shari’a a cikin harshen larabci; duk suna koyar da Shari’ar ne da harshen Turanci. Don haka, masana kimiyya bari suma su bincika wannan batun,” inji shi.