Jonathan Ya Shawarci Shugaba Buhari Kan Matakin Da Zai Dauka Ga Maharansa

Tsohon Shugaban Kasa, Goodluck Jonathan ya yi kira ga Gwamnatin Tarayya karkashin jagorancin Muhammadu Buhari da ta kama tare da tsananta wa ‘yan bindigar da suka kai hari gidansa a Otuoke, Jihar Bayelsa.

Kamfanin dillancin labarai na Naija News ta ba da rahoton cewa, tsohon shugaban bai sami rauni ba a harin wanda mutane da yawa ke zargin cewa ana son ne kashe shi.

Wani jami’in tsaro da aka sanya a gidan tsohon shugaban kasar ya mutu a harin amma ‘yan sanda basu fitar da sanarwa ba tukunna.

Da yake jawabi yayin da yake jagorantar masu juyayi a wurin da aka kai harin ranar Juma’a, Jonathan ya godewa ‘yan Najeriya kan nuna hadin kai da juyayi bayan harin da aka yi wa gidansa a ranar Kirsimeti.

Ya kuma yaba wa rundunar sojojin Najeriya saboda yunkuri da suka yi na gamewa da munsayar wuta da maharan a cikin wani mummunan artabu da ya yi sanadiyar mutuwar soja guda.

Tsohon shugaban kasar ya lura cewa da yawa daga cikin ‘yan Najeriya da suka hada da Shugaba Buhari, Gwamnonin jihohi da shugabannin jam’iyyun siyasa har ma da ‘yan kasashen waje sun je sun ziyarce shi, wasu kuma sun kira don nuna juyayi da kan yanayin harin.

Jonathan ya kuma yi kira ga hukumomin tsaro a karkashin jagorancin shugaba Muhammadu buhari da su kama wadanda suka aiwatar da wannan harin da kuma tabbatar da cewa irin wannan harin kunar bakin wake bai sake faruwa ba a cikin harabarsa ko wani wuri a cikin kasar ba.

Manyan Labarai daga Jaridun Najeriya ta ranar Litini, 29 ga Watan Yuli, Shekara ta 2019

Wadannan ne Manyan Labarai ta Jaridun Najeriya a yau Litini, 29 ga Watan Yuli, 2019

1. 2023: Dalilin da ya sa ya kamata Buhari ya mika mulki ga Kudu – Fasto Bakare

Babban Fasto da ki wakilcin Ikilisiyar Latter Rain Assembly, Tunde Bakare, ya shawarci Shugaba Muhammadu Buhari da mika shugabancin kasar Najeriya ga ‘yan Kudu a shekarar 2023 da ke gabatowa.

Babban malamin ya bayyana hakan ne ga manema labaran The Sun, da cewa ba za a bar arewa kadai da ci gaba da mulkin sauran al’umma ba har abada.

2. Osinbajo ya Ziyarci Iyalin marigayi mai daraja Owolabi

A ranar Lahadi da ta gabata, Mataimakin shugaban kasa, Yemi Osinbajo ya kai ziyara ga iyayen marigayi Precious Owolabi.

Naija News ta ruwaito a baya da cewa Owolabi, wanda ya kasance mai rahoto tare da gidan talabijin na Channels TV, ya mutu a yayin wata arangamar da ta gudana tsakanin mambobin kungiyar Islamic Movement of Nigeria (IMN) wanda kuma aka fi sani da Shi’a da kuma jami’an ‘yan sanda na Najeriya.

3. Nnamdi Kanu Ya Bayyana Wanda ya bada umarnin a tsananta masa

Shugaban kungiyar ‘Yan asalin yankin Biafra (IPOB), Nnamdi Kanu, ya zargi babban jami’in Burtaniya da sanya hannu a neman kisansa.

Najia News Hausa ta fahimta da cewa Nnamdi ya bayyana hakan ne a wata rahoto da ya bayar akan Gidan Radiyon Biafra a ranar Asabar da ta gabata.

4. Dangote na shirye don zuba Jarin Biliyan N288 ga tsarafa Madara a kasar

Jagoran kamfanin Dangote, Aliko Dangote, ya bayyana shirin kashe dala biliyan (N288 biliyan) a harkar samar da tsarafa madara ga tsawon shekaru Uku ta gaba.

Naija News ta fahimci cewa Dangote zai mallaki shanaye 50,000 nan da shekarar 2019, sannan zai samar da lita miliyan 500 na madara a kowace shekara.

5. ‘Yan Shi’a Sun yi barazanar ci gaba da yin Zanga-zanga duk da katangewa da aka masu

Wani mai magana da yawun kungiyar Harkar Musulunci ta Najeriya (IMN) da aka fi sani da suna Shi’a, ya mayar da martani game da dokar katangewa da Gwamnatin Tarayya ta bayar game da zanga-zangar da suke yi a birnin Abuja, bisa umarnin Kotun Koli.

Naija News ta fahimci cewa Kakakin wanda kamfanin dillancin labarai na Reuters sun bayyana da rashin gane da shi, ya fada da cewa duk da cewa kungiyar ba ta samu sanarwar daga kotu ba, amma ya ce zanga-zangar su zata ci gaba har sai an saki shugaban kungiyar su, Sheikh Ibrahim El-Zakzaky.

6. Gwamnonin Kudu Maso Gabas na taron kofa kulle

Gwamnonin da suka fito daga yankin Kudu maso Gabashin Najeriya a ranar Lahadi sun gana akan matsalar rashin tsaro da ke addabar yankin.

Naija News ta samu gane da cewa taron yana gudana ne a gidan gwamnatin jihar da ke a Enugu, babban birni Jihar.

7. Sojojin Najeriya Sun Kashe Mutane 5, An Kama Wasu ‘Yan bindiga 4 A Kaduna

Runduna Sojojin Najeriya ta 1 Division sun sanar da kashe wasu ‘yan fashi biyar da kuma kame wasu mutane hudu a kananan hukumomin Chikun da Igabi ta jihar Kaduna.

Naija News ta fahimci cewa sojojin sun kama tare da kashe wasu ‘yan bindiga a wata zagaye da suka kai a yankunan da ke a cikin jihar.

8. Ka Kalubalanci jagorancin Yari, Jigon APC sun gayawa Matawalle

Wasu shugabannin da Jigo a Jam’iyyar APC ta jihar Zamfara sun yi kira ga gwamna Bello Matawalle da ya binciki gwamnatin tsohon Gwamnan Jihar, Abdulaziz Yari.

Kungiyar sun bayyana hakan ne ga Gwamnan a yayin wata zama da suka yi a Gusau a ranar Asabar din da ta gabata.

9. Ku bar ‘Yan Shi’a, Ku bi bayan makiyaya da Miyetti Allah – Ozekhome ya gayawa Buhari

Lauyan kundin tsarin mulki, Mike Ozekhome ya gargadi shugaba Muhammadu Buhari da ya tafi bayan Miyetti Allah da kuma Makiyaya Fulani da manta da zancen bin ‘yan Shi’a.

Ya furta hakan ne a lokacin da yake mayar da martani ga zancen da Gwamnatin Tarayya ke yi na batun daukar  matakin musanman na dakatar da hidimar ‘yan kungiyar Islamic Movement of Nigeria (IMN) wacce kuma aka fi sani da Shi’a.

Ka samu kari da cikakken Labaran Najeriya a shafin NaijaNewsHausa

‘Yan Hari da Bindiga sun sace Matafiya 28 a Jihar Ondo (Kalli bidiyon kan hanyar da suke aiwatar da hakan)

Wasu ‘Yan Hari da Bindiga da har yanzu ba a gane da su ba, a ranar Talata da ta gabata sun sace kimanin mutane 28, matafiya da ke kan tafiyar a wata hanya da ke a Ado-Akure, Jihar Ondo.

Bisa rahoton da aka bayar ga Naija News Hausa, mazaunan shiyar sun bayyana da cewa ‘yan harin sun ci nasara da hakan ne bayan da suka gana da matafiya cikin motoci biyu manya, guda mai girman daukan mutane 18, dayan kuma mai kujera 9.

An bayyana da cewa yanayin lalacewar hanyar ne ya sa maharan suka sami sauki da nasarar tare motocin.

An gabatar da zargin matsalar hanyar ne a wata bidiyo da aka samar da shi a layin yanar gizon nishadi ta twitter, a tabbacin cewa domin rashin kyan hanyar, ‘yan hari da makami kan katange matafiya a kan hanyar su kuma sace mutane a kowane lokaci da suka sami damar haka.

Kalli bidiyon hanyar a kasa;

Sabuwa: An sace babban Malamin Makarantar Jami’a a Jalingo

Da safiyar yau Talata, 30 ga watan Afrilu, Naija News Hausa ta karbi rahoto da cewa wasu ‘yan hari da bindiga da ba a gane da su ba sun sace Mista Sanusi Sa’ad, mataimakin Rajistra na Makarantan Jami’a babba na Jihar Taraba da ke a Jalingo.

Bisa ga rahoton da aka bayar ga manema labarai, abin ya faru ne a missalin karfe daya (1am) na safiyar ranar yau, Talata, 30 ga watan Afrilu 2019, anan gidan shi da ke a mazaunin Malaman makarantar Jami’ar.

Naija News Hausa ta samun tabbacin hakan ne bisa bayanin da Ciyaman na Kungiyar Malaman Makarantar Jami’a babba na Jihar Taraba, Dakta Samuel Shikaa, ya bayar ga manema labaran Punch da ke a Jalingo akan wayar Salula.

A fadin Dakta Shikaa, ya bayyana da cewa ‘yan harin sun fada cikin gidan Mista Sanusi ne ta kofar bayar gidan, suka kuma sace shi ba da sanin kowa ba ko ta ina suka tafi da shi.

A halin yanzu Babban Makarantar Jami’ar Taraba a karkashin kungiyar ASUU na cikin yajin aiki akan matsalar rashin tsaro ta musanman da babu shi a Jihar.

Amma dai, Kwamishanan Jami’an tsaron ‘yan sandan Jihar Taraba, Mista Alkasim Sanusi, a yayin da yake kafa rukunin tsaron ‘Operation Puff Adder’, ya gargadi ‘yan hari da makami da ‘yan ta’addan Jihar Taraba da janyewa daga hare-haren da suke yi a Jihar, ya kuma yi barazanar cewa idan har suka dage basu bar hakan ba, zai tabbatar da cewa ya tsananta masu da ganin cewa ya magance su.

Karanta wannan kuma: Sheikh El-Zakzaky da Matarsa na bukatan mu tafi dasu kasar Turai don karin kulawa – Dakta Kazim Dhalla

Kimanin Mutane 36 ‘yan Ta’adda suka kashe a wata sabuwar hari a Jihar Katsina

Hukumar ‘yan Sandan Najeriya da ke a Karamar Hukumar Kankara ta Jihar Katsina sun gabatar da wata hari da mahara da makami suka kai a kauyan Tsamiyar Jino, inda suka kashe kimanin mutane 14, kamar yadda aka bayar ga manema labarai.

Ko da shike mutanen kauyan sun bayar ga manema labarai da cewa lallai mutane 36 ne maharan suka kashe a harin, amma jami’an tsaro sun bayar da cewa mutane 14 ne kawai suka gano a gawakin su; Mutum bakwai daga cikin ‘yan ta’addan, mutum bakwai kuma daga cikin Hadadiyar Kungiyar ‘Yan bangan yankin da suka bayar da kansu don tsaron Kasa.
An bayar ne da cewa al’amarin ya faru ne a ranar Lahadi da ta gabata bayan da wasu ‘yan banga suka kashe wani dan ta’adda da ake ce da shi Baban Kusa.
“Wannan itace sanadiyar mayar da martani da farmaki da ‘yan ta’addan suka fado wa kauyan da hari” inji shi.

Bisa bayanin wani, ya ce “Mutane 27 aka kashe a Unguwar Rabo, Takwas kuma a Unguwar Sarkin Aiki shi kuma guda a Center Na Ade.

Wakilin Unguwa Tsamiyar Jino, Jaafaru Bello Jino ya bayar ga manema labarai da cewa kimanin mutane 36 suka mutu a sakamakon hari.

“Muna tsoron shiga daji don dauko gawakin wadanda aka kashe wajen harin don mu yi masu zana’iza a hayar da ta dace.”
“Mun kira Jami’an tsaro don sanar masu da yanazin, amma ko da suka iso, suka kuma gane da yanayin, sai kawai suka koma ba tare da wata bayani ba” inji Jino.

Kakakin Yada Yawun Jami’an tsaron ‘yan sandan yankin, SP Gambo Isah, ya gabatar da cewa maharan sun shige cikin daji da ke kewayan don buya, sun kuma tafi da gawakin ‘yan uwansu da aka kashe zuwa cikin daji.

Naija News Hausa ta tuna da cewa shugaban Jami’an ‘yan sandan Najeriya, IGP Mohammed Adamu a ranar Lahadi da ta gabata ya bada umarni ga masu haƙa ma’addinai da ke aiki a Jihar da dakatar da ayukan su, don hukumar ta samu kadamar da kame ‘yan ta’addan da ke kai hare-hare a Jihar.

‘Yan Hari da Bindiga sun kashe kimanin Mutane fiye 13 a Jihar Zamfara

Mahara da Bindiga sun kai wata sabuwar hari a kauyuka biyu ta karamar hukumar Shinkafi a Jihar Zamfara ranar Lahadi da ta gabata.

Naija News Hausa ta gane da cewa kusan mutane goma sha shidda ne ‘yan harin suka kashe a kauyan Kursasa da Kurya a nan karamar hukumar Shinkafi, Zamfara.

Usman Garba, wani mazaunin kauyan Kursasa, ya gabatar ga manema labarai da cewa ‘yan harin sun fada wa kauyukan ne a missalin karfe goma (10PM) na daren ranar Lahadi, 31 ga watan Maris 2019 da ya gabata.

Ya bayyana da cewa ‘yan harin sun shigo ne kauyan da mugayan makamai da bindigogi.

“An take suka kashe mutane 9 a nan kauyan Kurkusa da kuma yi wa mutane da dama raunuka da harsasun bindiga” inji Usman.

“Bayan da kuma suka gama da kauyan Kurkusa, sai suka kara gaba zuwa kauyan Kurya inda suka kashe kimanin mutane bakwai a nan take, hade ma da ‘yan banga da suka fito don ganawar wuta da su”

Usman ya kara bayar da cewa da abin yayi zafi ‘yan bangan shiyar Kansas da kuma Kurya sun hada kai da ganawar wuta da ‘yan ta’addan kuma sun samu kashe daya daga cikin ‘yan harin.

Mun ruwaito a baya a Naija News Hausa da cewa ‘Yan Hari da bindiga sun hari shiyar Rigasa ta Jihar Kaduna a ranar Alhamis 28 ga watan Maris 2019 da ta gabata, Inda suka kashe wani mutum da kuma sace matarsa.

‘Yan ta’addan sun fada wa yankin Rigasa da hari ne, suka kuma kashe Malam Abdul’azeez bayan nan suka sace matar tasa kuma. kamar yadda aka baiwa manema labarai.

Usman, a cikin bayanin sa ya bukaci hukumomin tsaro da su taimaka masu da tsaro ta gaske don magance matsalar mahara a yankin su.

Ko da shike an bayyana da cewa Gwamnatin Tarayya ta bada umarnin watsar da Rundunar Tsaron kasa a dukan yankin Zamfara da ‘yan hari da makami ke kai wa farmaki.

‘Yan Hari sun saki Yahaya Lau bayan da suka karbi Miliyan Biyar

Mun gabatar a Naija News Hausa a wata sanarwa a baya da cewa ‘yan hari da bindiga sun sace Alhaji Yahaya Lau.

Alhaji Yahaya babban Ma’aikacin Gwamnati ne a Jihar Taraba. ‘Yan hari da bindiga sun sace shi ne ‘yan kwanaki Ukku da suka gabata a nan Jihar Taraba.

Mun samu rahoto da safiyar nan a Naija News Hausa da cewa ‘yan Hari da makamin sun saki Yahaya a missalin karfe Goma (10:30PM) na daren ranar Lahadi da ta wuce.

Daya daga cikin Iyalan Alhaji Yahaya ya bayar ga manema labarai da cewa sun biya kudi naira Miliyan biyar ga ‘yan ta’addan kamin suka saki Alhaji.

“Mun kai kudi naira Miliyan Biyar N5m a cikin wata doron daji da ke kusa da kauyan Kwando, a karamar hukumar Ardo-Kola ta Jihar Taraba missalin karfe 10 na dare kamin suka sake shi”

A kara bayyana ga manema labarai da cewa ‘yan harin, a ranar da suka sace Alhaji Yahaya, sun dauke naira Miliyan biyar a gidan sa.

Ko da shike a halin yanzu an sake shi, an kuma mayar masa da wayoyin salulan sa guda biyu da aka kwace, kamar yadda aka bayar a labarai.

Mun ruwaito a Naija News Hausa a baya da cewa Mahara da Makami sun sace Ubandoma, tsohon Ciyaman na Kungiyar Alkalan Jalingo.

Mahara da bindiga sun kai wata sabuwar hari a Jihar Kaduna

‘Yan Hari da bindiga a Jihar Kaduna ranar Alhamis 28 ga watan Maris 2019 sun hari shiyar Rigasa, a Jihar Kaduna, inda suka kashe wani mutum da kuma sace matarsa.

‘Yan ta’addan sun fada wa yankin Rigasa da hari ne, suka kuma kashe Malam Abdul’azeez bayan nan suka sace matar tasa kuma. kamar yadda aka baiwa manema labarai.

Abin takaicin ya faru ne missalin safiyar ranar Alhamis da ta gabata a nan unguwar Karshen Kwalta ta yankin Rigasa.

Karanta wannan kuma: Wata ‘yar mace tayi hadarin mota har ga mutuwa a yayin da take kan hanyan zuwa wajen hidimar bautan kasa (NYSC).
Wani mazaunin unguwa guda da Malam Abdul’azeez, ko da shike bai gabatar da sunan sa ba wai don tsaro, amma ya bayyana ga manema labarai da cewa lallai ‘yan hari sun fada wa unguwar su ne da hari suka kuma sace Matan mutumin bayan da suka kashe mijin ta.

“Abdul’azeez Tela ne, yana kuma dinkin Kaftani ne Maza a nan shiyar tamu” inji bayanin mutumin.

Ya kara da cewa Matar Abdul’azeez na da jariri da take baiwa mama, watau ‘nono’ a wannan lokacin da abin ya faru. “Wannan abin ya sanya mu duka cikin wani yanayi a unguwar mu. harin ba mai kyau bane ko kadan” inji shi.

“Muna neman tsaro kwarai da gaske a shiyar mu, hare-hare na kara yawa a kowani rana”

Ya gabatar da cewa sun riga sun yi zana’izar Abdul’azeez bisa ga dokar Islam a bayyanar rana ta ranar Alhamis.

Ko da shike an bayar da cewa ‘yan harin sun yi kira a waya da bukatar a biya wasu kudade kamin su saki matar, amma kakakin yada labarai ga jami’an tsaron ‘yan sandan yankin, Yakubu Sabo, yayi alkawarin cewa zai gabatar da duk wata bayani da ta biyo baya idan ya samu kira daga maharan.

Mahara da Makami sun sace Ubandoma, tsohon Ciyaman na Kungiyar Alkalan Jalingo

A ranar Laraba da ta gabata, ‘yan hari da makami sun sace Mista Joel Ubandoma, Tsohon shugaban Kungiyar Alkalan Najeriya (NBA) ta yankin Jalingo.

Bincike ta bayar da cewa an sace Ubandoma ne a nan gidan sa da ke a unguwar Mayo-Dassa ta Jalingo, missalin karfe daya (1:00AM) na safiyar ranar Laraba, 27 ga watan Maris da ya gabata, kamar yadda aka bayar ga manema labarai.

Mista Boniface Iorkumbur, Sakataren Kungiyar, ya bayyana da bada tabbacin harin ga manema labarai da cewa lallai lamarin da gaske ce. “Lallai ‘yan hari sun sace Mista Joel, abin ya jijjiga mu kwarai da gaske. Mun kuma yi addu’a da cewa Allah zai kubutar da shi”

“Mun tashi ne da safiyar nan da wannan labarin bakin ciki, da cewa an sace dan uwan mu”

“Mun riga mun yi kira ga ‘yan kungiyar mu da yin addu’a da fatan cewa Allah zai kubutar da shi, ya kuma sa an sake shi ba tare da wata matsala ba. Muna kuma kira ga jami’an tsaro da su yi kokarin taimaka da bincike ko watakila su iya ribato Mista Joel” inji Boniface, a bayanin shi da manema labaran NAN.

Iyalan Mista Joel sun bayar da cewa basu karbi wata kira ba tukunnan tun lokacin da aka sace shi.

Kakakin yada labarai ga Jami’an tsaron ‘yan sandan yankin, ASP David Misal, ya bayar da cewa zasu sanar da duk wata karin bayani akan binciken su game da harin.

Karanta wannan kuma: An kashe wani garin gwada karfin maganin bindiga

‘Yan Hari da makami sun sace Matan Alkali Sulaiman a Jihar Nasarawa

‘Yan Hari da makami a Jihar Nasarawa sun hari Suleiman Abubakar, Ciyaman na Hukumar Alkalan kasar Najeriya ta Jihar Nasarawa (NUJ), sun kuma sace matarsa, Yahanasu Abubakar.

A bayanin Suleiman da kungiyar manema labaran Najeriya, ya bayyana da cewa abin ya faru ne missalin karfe bakwai na maraicen (7:00PM) ranar Laraba da ta gabata a da ta bi Gudi zuwa Garaku, a nan karamar hukumar Akwanga.

“Maharan sun harbi motar Hukumar mu da muke tafiya da ita daga shiyar Keffi a inda matar ta sa ta je don ta yi rajistan sunan ta ga hidimar bautar kasa (NYSC)” inji Sulaiman.

Ya kara da cewa motar su ta fada ga wata babban rami bayar da ‘yan harin suka harbi motar. “Da suka ga motar ta lakke a rami, a gaggauce sai suka haro motar da sace mata na, matar dan gidan majalisar Jihar da muka taimaka wa da dauka hade da wasu mata biyu da ke cikin wata mota da ke biye da mu kuma” inji shi.

Ofisan Jami’an ‘yan sandan yankin, ASP Samaila Usman, watau Kakakin yada yawun jami’an tsaron, ya bayyana da cewa hukumar su sun watsar da darukan tsaro a shiyar da abin ya faru don ribato rayukar matan da aka kame.

Mun ruwaito a Naija News Hausa a baya da cewa Wasu Mahara da Makami sun sace wani Firist na Ikklisiyar Katolika da ke a Jihar Kaduna.