Connect with us

Uncategorized

Fada bai hana gaisuwa! Kalli Gwamnan Kano, Ganduje da Sarki Sanusi a Sallar Eid-Al-Fitr

Published

on

at

Duk da irin jayayya da matsar da ke tsakanin Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Ganduje da Mai Martaba Muhammad Sanusi II, Naija News Hausa ta gano da hotonunan su biyu a lokacin da suka gana a Masalacin Idi, a bayan sallar Eid Al-Fitr da aka yi a ranar Talata da ta gabata a Jihar.

Wannan ya biyo ne bayan da a ranar Talata da ta wuce, Hukumar Bincike da yaki da cin hanci da rashawa ta Jihar Kano ta bukaci cewa a tsige Sarki Muhammadu Sanusi II daga sarautar Jihar Kano, bisa wata laifin makirci da cin hanci da aka gane da shi a Jihar.

Ka tuna cewa mun ruwaito a Naija News Hausa a baya cewa Gwamnan Jihar Kano ya rabar da kujerar sarauta Kano ga yanki 5, hade da ta da wadda Sanusi ke jagoranci.

A bayan wadannan matsalolin da ke tsakanin manya biyun ne aka gano Abdullahi Ganduje da Muhammadu Sanusi na gaisawa da juna a masallacin Eid, bayan da aka kamala hidimar sallah.

Kalli hotuna a kasa;