Connect with us

Uncategorized

Ganduje: An kara Kujerar Sarauta Biyar (5) a Jihar Kano

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Ganduje, ya ba da izinin amincewa da kudurin da Majalisar Dokokin Jihar Kano ta dauka a kan rabar da kujerar martaba na Sarakai a Jihar.

Mun Fahimta a Naija News Hausa cewa wannan ya biyo ne bayan Gwamnan ya yi alwashin cewa zai bada hadin kai ga tafiyar da duk abinda Majalisar Wakilan Jihar suka gabatar da shi a gabansa.

A halin yanzu, Jihar Kano ta kasance da rukunin Kujerar Sarauta Biyar, suna kamar haka; Kano, Rano, Gaya, Karaye da Bichi. Wannan matakin ya rage yanki da wadiyar kujerar sarautan Muhammadu Sanusi, Sarkin Kano.

Hakan ya faru ne bayan da Majalisar Dokokin Jihar Kano a ranar Laraba da ta wuce, suka gabatar da dokar amince da gyaran Dokar kananan Hukumomi Jihar Kano.

Kwamitin sun amince da cewa samar da karin kujerar Sarauta a Jihar Kano zai taimaka wajen samar da ayuka, rage jayayya, da kuma rikice-rikicen tsakanin al’ummar Kano.

KARANTA WANNAN KUMA; ‘Yan Hari da Makami sun Kashe wani Sarki a Jihar Sokoto