Connect with us

Labaran Najeriya

Manyan Labarai daga Jaridun Najeriya ta ranar Laraba, 7 ga Watan Agusta, Shekara ta 2019

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Wadannan ne Manyan Labarai ta Jaridun Najeriya a yau Laraba, 7 ga Watan Agusta, 2019

1. Buhari ya bayyana ranar Rantsar da sabbin Ministoci

Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya gabatar da ranar Laraba, 21 ga watan Agusta, 2019, don rantsar da sabbin Ministoci.

Naija News ta fahimta da wannan sanarwan ne a wata sako da aka bayar a layin yanar gizo ta Twitter, a ranar Talata, 6 ga Agusta da ta wuce.

2. Hukumar DSS ta Nemi Umurnin Kotu don tsare Sowore a Tsawon kwanaki 90

Hukumar Bincike da Tsari ta Jiha da Jiha (DSS), ta nemi dama daga kotu don tsare Omoyele Sowore, jagoran zanga-zangar neman juyin mulki, a tsawon kwanaki 90.

Ka tuna da cewa Hukumar DSS ta kame dan takaran kujerar shugaban kasar ne a zaben 2019, tun ranar Asabar da ta gabata.

3. Akeredolu ya hana Ma’aikatansa da Bayanin a Fili

Gwamnan jihar Ondo, Oluwarotimi Akeredolu ya umarci ma’aikatan gwamnatin jihar da su daina mayar da martani ga zantutuka ko wata kalamai, ko sanarwa game da ‘batun da ya shafi rikicin filaye.’

Wannan biyo ne bayan da aka kafa kwamitin kwamitin da zai binciki wata rikicin da ta kan filaye tsakanin jama’ar Araromi Obu da Ikale (Ago Alaye).

4. Daliban Jami’a ta Abubakar Tafawa Balewa sun mutu a yankewar Gada

Bayan yankewar Gada Sakamakon ruwan sama mai karfin gaske da ya afku a jami’ar Abubakar Tafawa Balewa, jihar Bauchi, an ce wasu daliban sun mutu.

Bisa rahoton da aka bayar, Naija News Hausa ta fahimta da cewa gadar ta yanke ne sakamakon yawar ruwan sama, wanda ya kai ga sanadiyar mutuwa da bacewar wasu dalibai a yayin da suke dawowa daga karatun daga ajin su zuwa masaukin su.”

5. Reno ya la’anci hukumar EFCC da rashin tsige Shugaba Buhari bisa sakamakon WAEC

Tsohon ma’akaci ga tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan, Reno Omokri, ya kwatanta Shugaba Muhammadu Buhari da Yahoo Boys a yayin da yake mayar da martani game da jirga-jirgan takardar shaidar jarabawan WAEC ta Buhari.

Omokri ya la’anci Hukumar da kamun Yahoo Boys da ke amfani da bayanai na karya don cutar mutane, amma da barin shugaba Buhari duk da cewa ya gabatar da takardann karya don yaudarar ‘yan Najeriya.

6. Ku Saki Sowore Nan da nan – Shugaban PDP ya gayawa Buhari

Shugaban jam’iyyar Dimokradiyya (PDP), babbar jam’iyyar adawa a Najeriya, Uche Secondus, ya bukaci shugaban kasa Muhammadu Buhari da ya bayar da umarnin sakin Omoyele Sowore nan da nan.

Naija News ta bayar da rahoton cewa, shugaban PDP ya yi wannan kiran ne a Yola, babban birnin jihar Adamawa a arewacin Najeriya ranar Talata, a lokacin da ya kai ziyarar ta’aziya ga gwamna Ahmadu Fintiri akan rasuwar mahaifinsa, Umaru Badami.

7. Hukumar INEC ta Bayyana yawan Karar Kotu da take gudanarwa

Hukumar gudanar da hidimar Zaben kasar Najeriya (INEC) ta zargi jam’iyyun siyasar kasar saboda yawan korafin da kotu ta yi game da batun zaben 2019.

A cewar shugaban hukumar, Farfesa Mahmood Yakubu, ya bayyana da cewa sama da kara 1,600 aka kai hukumar su a Kotu dangane da babban zaben shekarar 2019.

8. Falana ya gargadi Gwamnatin Tarayyar akan cajin Sowore zuwa Kotu

Femi Falana, babban maishawarci da fatawa a Najeriya (SAN), ya kalubalanci Gwamnatin Tarayya game da gurfanar da tuhumar da ake wa Omoyele Sowore, da cewa wannan zai zan babban kuskure idan har ta yi hakan.

Ka tuna cewa jami’an Ma’aikatar DSS sun kama Sowore, shugaba da kuma jagorar kungiyar #RevolutionNow tun Asabar bayan an zarge shi da yin barazana ga zaman lafiyar kasa.

Ka sami kari da cikakken Labaran Najeriya a shafin NaijaNewsHausa