Connect with us

Labaran Najeriya

Manyan Labarai daga Jaridun Najeriya ta ranar Litini, 16 ga Watan Satunba, Shekara ta 2019

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Wadannan ne Manyan Labarai ta Jaridun Najeriya a yau Litini, 16 ga Watan Satunba, 2019

1. Xenophobia: Shugaban kasar South Afirka na shirin Aika da Wakilan musanman ga Shugaba Buhari, tare da wasu

Shugaban kasar South Afirka, Cyril Ramaphosa, na a shirye a yayin da yake batun aika da jakadu na musamman ga shugaban kasar Najeriya Muhammadu Buhari da sauran shugabannin Afirka da dama kan harin ta’addancin da ‘yan kasar suka yi a kwanakin baya.

Bisa rahoton da News24 ta bayara, Wakilan musamman za su isar da sakon ne ga shugabannin kasashen Afrika da gwamnatoci da dama a fadin Afirka.

2. Biafra: Shugaban IPOB, Nnamdi Kanu zai gana da jami’an Majalisar Dinkin Duniya ranar Talata

Jagoran kungiyar ‘Yan asalin yankin Biafra (IPOB) a ranar Talata, 17 ga Satumbar, zai gana da jami’an Majalisar Dinkin Duniya a ofishin sa da ke a Geneva, a kasar Switzerland.

Naija News ta fahimta da hakan ne bisa wata gabatarwa da Magatakardar kasar, ya bayar ga manema labarai.

3. ‘Yan Sanda Sun Ba da Gargadi mai Karfi ga Daliban FUOYE

‘Yan sanda a Jihar Ekiti sun yi gargadin cewa daliban Jami’ar Tarayya, Oye Ekiti (FUOYE) da su guji duk wani taron jama’a da zai iya haifar da tashin hankalai a kasar.

Naija News ta samu sanin cewa rundunar ‘yan sanda ta jihar yayin da take bayar da gargadin, ta jaddada cewa daliban su guji duk wani nau’in zanga-zanga, musamman zanga-zangar da aka danganta da kisan dalibai biyu a Jami’ar kwanar baya.

4. Kungiyar CUPP ta Bayyana shirin Gwamnatin Tarayya kan karkashiyar makircin da ta ke yi kan Hukunci zaben Shugaban Kasa

Kungiyar Hadin Kan Jam’iyyun Siyasa (CUPP) ta zargi Gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari da shirin makirci hade da alkalan Kotun koli gabanin hukuncin karar da Atiku Abubakar ya yi game da hukuncin Kotun Shugaban Kasa Petition Tribunal (PEPT).

Naija News ta tuno cewa Kungiyar ta PEPT ta yi watsi da karar da Atiku Abubakar na Jam’iyyar PDP ya kalubalanci nasarar Shugaba Buhari da shi a zaben 2019.

5. Tsohon Gwamnan Benue, Suswam na batun barin Jam’iyyar sa

Rahoton da ke isa ga Naija News ya nuna cewa tsohon gwamnan jihar Benue da Sanata mai wakiltar mazabar Benue ta Gabas ta Tsakiya, Gabriel Suswam zai iya koma ga Jam’iyyar All Progressives Congress a cikin kankanin lokaci.

Wata majiya ne ta bayyana hakan a wata sanarwa ga manema labaran Naija News.

6. Ku gayawa Buhari ya yi biyayya da Umurnin Kotu – SERAP ta gayawa AGF Malami

Kungiyar ‘Socio-Economic rights and Accountability Project (SERAP) ta bukaci Attorney Janar na Tarayya da Ministan Shari’a, Abukabar Malami, da su ba Shugaba Muhammadu Buhari shawarar biyayya ga hukuncin kotu.

SERAP ta yada hakan ne ga zancen hukuncin da mai shari’a Chuka Austine Obiozor ya bayar na ba da umarnin sakin bayanan biyan dukan kudaden da ya shafi aikin wutar lantarki da kamfanoni tun 1999.

7. Xenophobia: Abin da ya kamata Gwamnatin Tarayya ta yi ga gwamnatin South Afirka – Akinyemi

Farfesa Bolaji Akinyemi, tsohon Ministan Harkokin Waje, ya yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta ja Gwamnatin kasar South Afirka zuwa Kotun Duniya ta kasa saboda rashin kulawa da ‘yan Najeriyar da ke zaune a kasar South Afirka.

Ya fadi wannan ne sakamakon harin ta’addanci d ‘yan kasar suka yi wa ‘yan Najeriya da ke zaune a can.

Ka samu kari da cikakken Labaran Najeriya a shafin Naija News Hausa