Connect with us

Uncategorized

#RevolutionNow: A Karshe Hukumar DSS Ta Saki Sowore

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

A Karshe dai, Ma’aikatar hukumar tsaron Jiha ta Kasa (DSS) ta saki Omoyele Sowore, dan jaridan Sahara Reporters, da kuma jagoran zanga-zangar neman juyin juya hali, wadda aka fi sani da #RevolutionNow.

Naija News ta rahoto cewa an saki Sowore ne a ranar alhamis da yamma bayan ya share tsawon kwanaki 124 a tsare.

Wannan rahoton ya bayyana ne a yanar gizo, daga sanarwan Sahara Reporters, wacce Sowore da kansa ya mallaka.

Naija News Hausa ta ruwaito a baya da cewa wata Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta umarci hukumar DSS da ta saki jagoran zanga-zangar #RevolutionNow, Omoyele Sowore, da Olawale Bakare a cikin awanni 24.

Mai shari’ar, Ijeoma Ojukwu, wadda ta ba da umarnin ta kuma bayar da tarar N100, 000 akan DSS kan jinkirin da hukumar tayi wajen sakin Sowore da Olawale Bakare.