Connect with us

Uncategorized

Ba Damar Amfani Da Wayar Salula Idan Kun Isa Wajen Da Sojoji Ke Tsaro – Rundunar Sojojin Najeriya

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Bamu amince da amsa kira kan Wayar Salula ba inda an isa kusa da inda Sojoji ke tsari da binciken motoci, in ji wani babban jami’in sojojin Najeriya a ranar Litinin.

“Matakin tsaro ne lokacin da ka kusanto wurin bincike, ba kada damar yin waya.” inji Babban jami’in sojan Najeriya, Major Janar Usman Mohammed, a ranar Litinin da ta gabata.

“Abin kula shine idan kuna yin waya kusa da inda sojoji ke tsaro da bincike, wannan alama ce ko ta tattaunawa da wasu miyagun mutane. Ko kuma amfani wayar don gudanar da wata mugun shiri kan wasu na’urori.” Inji Jami’in.

Mohammed ya ce dokar bata zama sananne ga ‘yan Najeriya ba.

“Dokar tana a ko’ina! mutanen da suka ziyarci ƙasar waje sun san da cewa ba ka da damar yin amfani da waya lokacin da za ku kusanci Sojoji da ke a kan tsaro.”

Ya kara da cewa Hukumar Tsaron Gida ta Najeriya a shekaru bisa shekaru goma ta na fuskantar matsin lamba daga rikicin Boko Haram, rikicin makiyaya da makiyaya, da kuma ‘yan garkuwa ta wahalar da hukumomin tsaro na kasar.

Naija News Hausa ta ruwaito a baya da cewa wasu ‘Yan Bindiga sun Kashe Mutane Hudu a Yayin Kallon Gasar Wasan Kwallon Kafa a Kaduna.

A wani rahoto da jaridar Daily Trust ta fitar, wacce Naija News Hausa ta samu a sanarwa, ta ce wasu mutane dauke da makamai sun harbe mutane hudu tare da raunata wasu hudu a wani hari a filin wasan kwallon kafa a kauyen Zunuruk na karamar hukumar Kaura a jihar Kaduna.

Rahoton ya bayyana da cewa Maharan sun kai hari ne a ranar Lahadin da ta wuce da yamma yayin da matasa suke kallon wata gasar kwallon kafa.