Connect with us

Uncategorized

Babbar Kotun Jihar Kano Ta Baiwa Ganduje Iko Kan Masarautar Jihar

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Babbar kotun jihar Kano ta amince da baiwa gwamnan jihar Kano, Alhaji Abdullahi Ganduje ikon cire duk wani sarki a cikin a bisa tsarin doka.

Mai shari’a A. T. Badamasi wanda ya sanar da haka a yau a Kotu bayan ya ki bayar da damar tsawaita karar umarnin  hana gwamna Abdullahi Umar Ganduje damar kutsa kai da kuma iko kan masarautar Kano.

Naija News Hausa ta fahimci cewa alkali da kuma mai ba da shawara ga masarautar a cikin kara mai lamba K/197/2019 ya roki kotun da ta ba da umarni tsawaita hana damar ga Ganduje har sai an cimma karshen sauraren karar.

Amma bisa ga hukuncin yau zai zama da cewa gwamna Ganduje a yanzu yana da damar yin amfani da dukkan ikon da yake da shi a ƙarƙashin sabuwar dokar Majalisar Masarautar Kano ta 2019.