Connect with us

Uncategorized

Majalisar Dattijai Ba za ta Zartar da Dokar Kalaman Kiyayya Ba – Shugaban Majalisa

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Shugaban majalisar dattijai ta Najeriya, Ahmed Lawan ya ce zauren majalisun dokokin kasar ba za su zartar da dokar yada kalaman kiyayya ba.

Wannan zancen ya biyo bayan koke-koke da zanga-zangar da aka yi kan kudirin kalaman kiyayya wadda Sanata Aliyu Sabi Abdullahi, mai wakilcin APC a jihar Neja ya gabatar.

Ku tuna, kamar yadda Naija News Hausa ta ruwaito a baya cewa Sanata Enyinnaya Abaribe ya ce, ‘Da Lai Mohammed ya mutu ko idan da a ce an kafa dokar kisa kan kalamun kiyayya tun wa’adin Jonathan’.

Abaribe ya mayar da martani game da dokar mutuwa ta hanyar ratayewa wanda ke a kunshe cikin wata sabuwar tsarin da Majalisar Dattawa ke kokarin kafawa.

Abaribe a cikin yada yawunsa ya haɗu da wasu ‘yan Najeriyar don ƙin amincewa da dokar.

Yace; “Idan da an riga an zartar da irin wannan dokar a lokacin mulkin tsohon Shugaba Goodluck Jonathan, da Ministan Yada Labarai da Al’adu, Lai Mohammed a yanzu ya mutu ko.”