Connect with us

Labaran Najeriya

APC: Shugaba Muhammadu Buhari ya sauka Jihar Kano

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Kamar yadda muka sanar a Naija News Hausa da cewa Jam’iyyar APC ta Jihar Kano sun gabatar da cewa shugaba Muhammadu Buhari zai ziyarci Jihar don gabatar da hidimar yakin neman zabe a yau Alhamis 31, ga Watan Janairu, 2019.

Mun sami rahoto da cewa shugaba Buhari ya sauka a Jihar yanzunan, kuma jami’an tsaro ‘yan sanda da rundunar sojojin na zagaye a Jihar, musanman a shiyar da shugaban kasan zai yi gabatarwar ralin.

Mun sami tabbacin wannan rahoton ne daga shafin nishadarwa ta Bashir Ahmed, Sakataren yada labaran musanman ga shugaba Muhammadu Buhari.

bayanin na kamar haka:

Mun ruwaito a Naija News Hausa da cewa Sabon Kakakin yada yawun Jami’an tsaron ‘yan Sandan Najeriya, Frank Mba ya bada tabbaci ga ‘yan Najeriya da cewa jami’un su zata samar da kyakyawar shiri na tsaro ga zaben tarayya da ke gaba.

Ko da shike bayan ya fadi hakan, wasu ‘yan Najeriya sun mayar da martani akan zancen sa da barazanar da jami’an ke yi na kafa tsaro ga zaben 2019.

Fadin na kamar haka a turance: “We will do everything humanly, operationally and administratively possible to ensure buhari wins the election” is what you meant to say?

Wani kuma ya mayar da martanin nasa kamar haka