Connect with us

Labaran Najeriya

Shugaba Muhammadu Buhari na ganawa da Manyan Shugabannan tsaron kasa

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Naija News Hausa ta karbi rahoto da ya bayyana da cewa shugaba Muhammadu Buhari a yau Alhamis, 11 ga watan Afrilu 2019, na zaman kofa kulle don tattaunawa da manyan shugabannan hukumomin tsaron kasar.

Zaman ta fara ne missalin karfe goma sha daya (11:00am) na safiyar yau a nan Fadar Shugaban Kasa ta Abuja, babban birnin Tarayyar kasar Najeriya.

Ko da shike ba a bayyana dalilin zaman gaugawan ba, amma muna hangen cewa zaman ba zai wuce akan matsalar hare-hare da kashe-kashen rayuka da ke gudana a kasar ba. Musanman a Arewacin kasar Najeriya.

Zamu sanar da sakamakon ganawar jin kadan da nan a shafin mu na Hausa.NaijaNews.Com

Karanta wannan kuma: Shahararrar ‘yar shirin fim a Kannywood, Hadiza Gabon ta sake fada da wata a fagen hadin fim.