Connect with us

Uncategorized

Karanta yadda Kocin Liverpool ya rattaba wa Messi bayan wasan su da Barcelona

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Naija News Hausa na da sanin cewa wasan kwallon kafa na UEFA Champions League tsakanin Barcelona da Liverpool da aka yi a daren ranar Laraba, 1 ga watan Mayu ya karshe ne 3 – 0, a yayin da Lionel Messi ya lashe ragar Liverpool da gwalagwalai 2, shi kuma tsohon dan wasan Liverpool na da, Suarez ya jefa gwal 1 a ragar tsohon kulob na shi.

Ko da shike dai, ‘yan wasan kwallon Liverpool sun taka rawar gani a wasan, amma basu da sa’ar gwal. Haka kuma ga ‘yan wasan Barcelona, su ma sun yi nasu kokarin, musanman ma sun dace da jefa gwalagwalai 3 ga ragar Liverpool a Filin kwallon wasan Camp Nou.

Kocin Liverpool, Jurgen Klopp, bayan da aka kamala wasan, manema labaran wasan kwallo sun bincike shi da bayani, ya kuma bayyana a cikin bayanin sa da cewa “Lallai wasar bai zama da mamaki ba a gareni, Messi shahararren dan wasa kwallo ne a dukan duniya, kowa ya san dashi, ya kuma nuna hakan a hadewar mu da su”

Kalli bayanin a Turance a layin Twitter;

“Bamu iya mun dakatar ko hana shi cin Firikik da ya buga ba, ba nan kade ba, ya nuna da cewa lallai shi kwararre ne a wasar. Mun yi iya kokarin mu da iyawarmu, amma wasar ta kare yada ta kare.” inji Klopp.

KARANTA WANNAN KUMA: Yafi Kyau da dacewa a Aurar da ‘ya Macce ko ‘Da Namiji da kankanin Shekaru – inji Akashat Ny’mat