Manyan Labarai daga Jaridun Najeriya ta ranar Talata, 30 ga Watan Yuli, Shekara ta 2019

Wadannan ne Manyan Labarai ta Jaridun Najeriya a yau Talata, 30 ga Watan Yuli, 2019

1. Boko Haram: Shugaba Buhari Ya mayar da martani game da mutane 60 da aka kashe

Bayan harin da aka yi wa masu makoki a wani taron jana’izar da ya gudana a jihar Borno, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 60, Shugaba Muhammadu Buhari ya la’anci da wannan matakin.

Shugaba Buhari ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ya bayar ta hannun mai magana da yawun sa, Garba Shehu, ya fada da tabbacin cewa za a kama ‘yan ta’addan da suka aikata kisan.

2. Rikicin Majalisar Edo: Obaseki ya ki bayar da sabon sanarwar

Gwamna Godwin Obaseki a ranar Litinin ya ce ba zai fitar da wata takaddar shelar sanarwa ba domin kafa majalisar dokokin jihar Edo ta bakwai.

Ya sanar da hakan ne yayin da yake mayar da martani kan wata rahoton da Shugaba Muhammadu Buhari ya bayar na umartan sa da gabatar da sabon shirin.

3. Abin da Dino Melaye ya fada Game da Tantancewar Ministoci

Sanatan da ke wakilcin maharabar yamma ta Kogi, Dino Melaye ya kalubalanci hidimar tantance sunayen ministocin da Majalisa ke yi ga marasa gabatar da jakar su.

Naija News ta fahimci cewa Sanata Dino a yayain da yake mayar da martani ga hidimar tantancewar, ya bayar da cewa tantancewar sunan Ministocin ya kasance da sauki a saboda abin bai cika da gaskiya ba bisa tsari.

4. Biafra: ‘Yan Kungiyar IPOB sunn bayyana lokacin da shugabansu Nnamdi Kanu zai dawo Najeriya

Kungiyar ‘Yan asalin yankin Biafra (IPOB) sun gabatar da cewa shugabansu Mazi Nnamdi Kanu zai dawo Najeriya nan ba da jimawa ba.

Mai magana da yawun kungiyar, Emma Powerful ya fada da cewa Kanu zai dawo Najeriya don shirin tsarafa da kuma tabbatar da kafa Biafra, “a yayin da wannan na cikin dalilin da yayi tafiya.

5. Yadda Aregbesola ya ba ni Albashinsa Shekaru 7 da suka gabata – Sanata Abbo

Sanata Elisha Ishaku Abbo, Sanata da ke wakilcin yankin Arewacin Adamawa a Jam’iyyar PDP, ya bayyana da cewa tsohon gwamnan jihar Osun, Rauf Aregbesola, ya taba tallafa mashi da albashin sa shekaru bakwai da suka gabata don tsayawa takara.

Dan majalisa ya bayyana wannan zancen ne a yayin da ake tantace jerin sunayan Ministoci da shugaba Buhari ya baiwa ‘yan majalisa.

6. INEC ta ki gabatar da shaidu don kalubalantar Jam’iyyar PDP

Hukumar gudanar da hidimar zaben Najeriya (INEC), ta sanar ga Kotun kara ta shugaban kasa da ke a birnin Tarayya, Abuja da cewa, ba zasu yi kira ga wani shaida ba kamar yadda jam’iyyar PDP ke bukata da su.

Naija News ta fahimci cewa Lauyan INEC, Yunus Usman (SAN) ne ya sanar da hakan a lokacin da aka bayyana a kotun da gabatar da hukunci akan karar.

7. Kotu ta sake daga sauraron takardar neman belin El-zakzaky har zuwa 5 ga watan Agusta

Babbar Kotun Jihar Kaduna ta dage sauraron karar da ake yi ga shugaban kungiyar ‘yan Shi’a, Ibrahim El-Zakzaky, don neman beli daga tsarewa.

Naija News ta fahimci cewa Mai shari’a Darius Khobo ya yi alkawarin gabatar da hukunci game da karar a ranar Litini 5 ga watan Agusta 2019.

8. NLC taki amincewa da Nadin Ngige A Matsayin Ministan Kwadago

Kungiyar kwadago ta Najeriya (NLC), ta bukaci shugaba Muhammadu Buhari da cewa kada sake nada Dokta Chris Ngige a matsayin Ministan kwadago da samar da ayyuka.

Naija News ta gane da cewa Kungiyar kwadago ta Najeriya ta dade da bayyana rashin amincewa da Ngige a matsayin shugaban ‘yan kwadago tun jagorancin sa ta farko a matsayin Minista.

Ka samu kari da cikakken Labaran Najeriya a NaijaNewsHausa