Connect with us

Labaran Najeriya

Manyan Labarai daga Jaridun Najeriya ta ranar Jumma’a, 8 ga Watan Nuwamba, Shekara ta 2019

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Wadannan ne Manyan Labarai ta Jaridun Najeriya a yau Jumma’a, 8 ga Watan Nuwamba, 2019

1. Sunaye da Matsayin Ma’aikatan Osinbajo Da Shugaba Buhari Ya Kora

Naija News ta samu cikakken jerin sunan ma’aikata ga Mataimakin Shugaban Kasa Yemi Osinbajo, wadanda kwanan nan Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya kore su daga ofishin mataimakin.

Ka tuna kamar yadda Naija News ta ruwaito a baya da cewa, Shugaban wanda a yanzu haka yake a Burtaniya don wata ziyarar sirri ya kori ma’aikata 35 da ke aiki a ofishin Mataimakin Shugaban kasar.

2. Kogi: Kotu ta Umarci INEC ta hada dan takarar SDP, Natasha Akpoti a Tsarin Zaben Kogi

Babbar Kotun Tarayya a Abuja ta ba da umarnin a sake dawo da Malama Natasha Akpoti, ‘yar takarar kujerar Gwamna Jihar Kogi zaben ranar 16 ga Nuwamba a karkashin jam’iyyar Social Democratic Party (SDP).

Mai shari’a Folashade Ogunbanjo-Giwa, ta ba da umarnin ga Hukumar Gudanar da Hidimar Zaben Kasa (INEC) yayin da ta zargi hukumar da daukar matakin da bai dace na kin amincewa da jam’iyyar da dan takararta a zaben.

3. Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta Hana EFCC, ICPC Da Kwace kadarorin ‘Yan Siyasa Da aka Kama da Cin hanci da Rashawa

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta haramtawa dukkanin hukumomin hana cin hanci da rashawa a kasar damar kwace kadarorin jami’an gwamnati da aka gane ko kuma kama da halin almundahana.

Naija News ta fahimci cewa an saki wannan umarni ne a cikin wata sabuwar doka wacce gwamnatin a yanzu ta riga ta watsar da labaran haka ga sanin al’umma.

4. Kotu ta yanke hukunci kan Belin Maina

Mai shari’a Okon Abang na Babbar Kotun Tarayya, Abuja, ya ki yin hukunci a kan belin tsohon Shugaban kungiyar ‘yan Fensho, Abdulrasheed Maina, wanda aka shigar.

Mai shari’ar, Abang wanda ya ce za a sanar da hukuncin ne a karshen aiki ranar Alhamis, ya danganta dalilin rashin hakan kuma ga nauyi da ke gaban kotun.

5. Lauyoyin Kasa Sun Zargi Shugaba Buhari Da Saba wa kundin Tsarin Mulkin Kasa kan Tafiyar ba tare da bai wa Osinbajo Shugabanci ba

Wani tsohon Mataimakin Shugaban Kungiyar Lauyoyin Kasa, Mista Litinin Ubani, ya yi Allah wadai da gazawar Shugaba Muhammadu Buhari ga mika mulki ga Mataimakin Shugaban kasa, Yemi Osinbajo, kafin ziyarar sirri da ya kai a Landan.

A bayanin Mista Ubani, ya ce Shugaba Buhari ya saba wa kundin tsarin mulkin kasar da kin mika jagoranci ga Osinbajo.

6. Eid-El-Maulud: Gwamnatin Tarayya Ta Bada Hutun Mauludi {Duba Kwanan Wata)

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta ayyana ranar Litinin a matsayin ranar hutu ta Jama’a a bikin tunawa da zagayowar Eid-El-Maulud wanda ya kasance ranar tunawa da haihuwar manzon Allah Muhammad.

Daraktan yada labarai da hulda da jama’a na ma’aikatar cikin gidan, Mista Mohammed Manga ne ya sanar da hakan a cikin wata sanarwa da aka bayar a ranar Alhamis a birnin tarayya, Abuja, a madadin Ministan Harkokin Cikin Gida, Ogbeni Rauf Aregbesola.

7. Gwamnatin Tarayya ta bada Umarnin Dakatar da Samar da Man Fetur zuwa tashoshin da akwai Boda

Gwamnatin tarayya kasa ta ba da umarni cewa bai kamata a shigar da kayayyakin da ya shafi man fetur a tashoshin da ke kusa kilomita 20km a kusa da yakunan da Boda yake ba.

An ba da wannan umarnin ne ta hannun kwantrola Janar na kwastomomin Najeriya, Hameed Ali, a cikin wata wasika wanda aka wallafa ranar 6 ga watan Nuwamba.

8. Afenifere sun Zargi Shugaba Buhari da Cin Mutuncin Ofishin Osinbajo

Yinka Odumakin, kakin yada yawun kungiyar gamayyar siyasa da Al’adar Yarabawa, Afenifere, sun lura da cewa an kuntata da ci mutuncin ofishin Mataimakin Shugaban Kasa, Yemi Osinbajo.

Odumakin a cikin gabatarwansa da ya fitar ya ce an yi riga an ci mutunci da kunyata Ofiishin Mataimakin Shugaban Kasar.

Ka samu Kari da Cikakken Labaran Najeriya a shafin Naija News Hausa