Connect with us

Uncategorized

DSS: An Bamu Miliyan Daya Don Dakatar Da Zanga-zangar sakin Sowore – Deji

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Naija News ta ruwaito a Manyan Labaran Jaridun Najeriya ta ranar Laraba da cewa Ma’aikatar hukumar tsaron kasa (DSS)  sun harba tiyagas da bindiga don tarwatsa masu zanga-zanga da suka afka wa ofishinta don neman sakin Omoyele Sowore.

Masu zanga-zangar, a karkashin jagorancin Deji Adeyanju, sun mamaye ofishin hukumar ne a Abuja domin neman a saki Sowore nan da nan.

Wannan matakin kungiyar ya biyo ne bayan da Lauyan Yaki da Daman bil adama, Femi Falana ya bayyana da cewa Omoyele Sowore, marubucin labarai na kamfanin dilancin Sahara da kuma jagoran #RevolutionNow ya cinma sharudan da ake bukata don belin sa.

Ka tuna a baya da cewa kungiyar Ci gaban Musulunci a kasa (IMN) wadda aka fi sani da suna ‘Yan Shi’a sun hari Gidan Majalisar Dokokin Kasar Najeriya a birnin Abuja da zanga-zangar neman a saki shugaban kungiyarsu, Sheikh Ibrahim El-Zakzaky da matarsa da aka kulle tun shekarun da suka gabata.

Naija News Hausa ta tuna da cewa zanga-zangar ya haifar da mumunar yanayi, a yayin da wani shugaban Jami’an Tsaro da wasu ‘yan Shi’a suka rasa rayukan su a lokacin.