Connect with us

Uncategorized

Mutane Takwas Sun Mutu Sakamakon Fashewar Gas a Katsina

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Wau Mutane takwas ‘yan gida guda sun mutu a ranar Asabar din da ta gabata a wani fashewar gas a karamar hukumar Danmusa da ke jihar Katsina.

Maƙwabta ga mutanen da abin ya faru da su sun sanar da wakilin kamfanin dilancin labarai ta PUNCH da cewa lamarin ya kashe mata uku ne da yara biyar.

Wata majiyar ta ce, ‘yan sanda da suka zo daga baya sun yi kokarin rushe katangar gidan don su samu damar shiga gidan, amma a wannan lokacin zuwar su ya yi latti saboda mutanen sun rigaya sun kone harma baka iya gane fuskarsu kuma.

Kakakin Rundunar ’Yan sandan Jihar Katsina, SP Isah Gambo, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa, “Gaskiya ne. ”

Haka kazalika wani dan uwa ga mutanen da abin ya shafa mai suna, Mai Yusuf Lawal, shi ma ya tabbatar da faruwar.

Ka tuna Naija News Hausa ta ruwaito a baya da cewa Kimanin mutane 28 sun kone kurmus fiye da gane wa a ya yin wata sabuwar hadarin wani mota da ya afku a kan babbar hanyar Ningi da ke jihar Bauchi.

“Wannan mummunan labari ne kuma abin bakin ciki ne ga mutane 28 daga dangi guda su mutu a hadari guda a cikin rana guda. Abin da bakin ciki a gaskiya.” inji Abdullahi Yamadi, dan uwa ga wadanda suka mutu a hadarin.