Connect with us

Uncategorized

#EidAlFitr2019: ‘Yan Sanda sun kame mutane 55 da suka tada fada a Jihar Bauchi

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Jami’an tsaron ‘Yan Sandan Bauchi a yau Alhamis, 6 ga watan Yuni 2019 sun kame mutane 55 da ake zargi da kasancewa a fadar da aka yi a ranar Laraba da ta wuce, wajen hidimar sallar Hawan Daushe.

Bisa bayanin kakakin yada yawun Jami’an tsaron Bauchi, DSP Kamal Datti Abubakar, ya bayyana da cewa hukumar su ta kame mutanen ne da kuma ribato makamai da ke a hannun su. Ya fada cewa fadar ya tashi ne a lokacin da ake hidimar Dubar, dadai lokacin da wakilan sauratar yankin Bauchi ke ziyarar Gwamnan Jihar, Bala Mohammed, a nan gidan gwamnatin Jihar da ke a Bauchi.

“Fadar ya tashi ne tsakanin wata kungiyar ‘yan farauta da ke biye da wakilin Darazo da kuma wata kungiya ta shiyar Duguri, a yayin da ake cikin hidimar Durbar.”

“A garin hakan ne aka kashe wani daga karamar hukumar Darazo mai suna Auwalu Sadau ‘M’, aka kuma yiwa Usama Musa daga shiyar Duguri a karamar hukumar Alkaleri da kuma Zakari Suleiman daga karamar hukumar Darazo, hade da wasu mutane 12 suka yi mugun raunuka sakamakon harin” inji DSP Kamal.

Ya kara da cewa hukumar Jami’an tsaron Bauchi sun riga sun lafar da fadar a jagorancin Operation Puff Adder.\

“Hukumar ta amshe makamai daga hannun mutane 55 da aka kame, an kuma haura da wadanda suka yi rauni a Asibitin ATBUTH don basu kulawa da musanman.”

Rahoto ta bayar da cewa Gwamnan Jihar, Bala Abdulkadir Mohammed ya riga ya ziyarci mutanen a asibiti, ya kuma gargadi al’ummar shiyar da kasance da zaman lafiya.

Mun ruwaito a baya a Naija News Hausa cewa Yan Hari da Bindiga sun kashe akalla mutane 16 a Ranar Sallar Eid-Al-Fitr a Zamfara