Connect with us

Labaran Najeriya

Manyan Labarai daga Jaridun Najeriya ta ranar Talata, 10 ga Watan Satunba, Shekara ta 2019

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Wadannan ne Manyan Labarai ta Jaridun Najeriya a yau Talata, 10 ga Watan Satunba, 2019

1. Xenophobia: Cikakkun Labaran Rahoton Wakilan Musamman ga Shugaba Buhari a South Afirka ya fito

Shugaban kasan Najeriya, Muhammadu Buhari ya karbi rahoto daga manzon musamman da ya aika zuwa kasar South Afirka sakamakon sabbin hare-hare kan ‘yan Najeriya a kasar.

Naija News ta tuno da sabbin hare-hare da aka fara yi a makon da ya gabata, wanda ya haifar da lalata shaguna da kaddarorin da ‘yan Najeriya da sauran’ yan kasashen waje ke da su a South Afirka.

2. IGP ya mayar da Martani game da shirin Hidimar ‘Yan Shi’a

Babban Sufeto-Janar na ‘yan sandan Najeriya, IGP Mohammed Adamu, ya yi rashin amincewa da zanga-zangar nuna adawa da kungiyar Harkar Musulunci ta Najeriya (IMN), wacce kuma aka sani da Shi’a ke shirin yi.

Duk da hukunci da Kotun Najeriya ta yanka ga Kungiyar, IMN ta dage da yin hidimar Ashura na shekara-shekara da suke yi a ranar Talata.

3. DSS ta bayyana tsare-tsaren Da Wasu Mutane ke yi tayar da Tanzoma a Najeriya

Ma’aikatar Ayyukan Tsaron Jiha-da-Jiha (DSS) ta fitar da wata sanarwa da ke cewa wasu mutane na kadamar da shirin tayar da tashin hankali a kasar.

Hukumar DSS ta bayyana ta bakin kakakin ta Peter Afunaya, da cewa ba za ta yi nadama ba a kokarin da ta ke na kare al’umar kasar.

4. Shugaba Buhari ya Ba da umarnin dawo da ‘Yan Najeriya Daga kasar South Afirka

Bayan harin ta’addancin da ‘yan Najeriya suka fuskanta a kasar South Afirka, Shugaba Muhammadu Buhari ya umarci Ministan Harkokin Waje, Geoffrey Onyeama, ya gana da hukumomin kasar kan yadda za a kawo karshen hare-haren ta’addancin da aka yiwa ‘yan Najeriya.

Shugaban ya kuma amince da dawowa da ‘yan Najeriya da ke son komawa Najeriya daga kasar.

5. Kotun Koli ta Tsige Orji Uzor Kalu na Jam’iyyar APC

Kotun sauraren kararraki ta Majalisar Tarayya da ta Jiha ta soke zaben Orji Uzor Kalu, Sanata mai wakiltar mazabar Abia ta Arewa a majalisar dattijan Najeriya.

Naija News ta ba da rahoton cewa Kotun daukaka kara ta kasa da na jihohi da ke zaune a jihar Abia sun soke zaben Kalu a ranar Litinin, 9 ga Satumba.

6. An kashe mutum daya, biyar suka jikkata a harin Xenophobic da aka yi a South Afirka

Mutum daya ya mutu, wasu biyar kuma suka jikkata a Johannesburg, babban birnin kasar South Afirka, a wani sabon harin ta’addanci da kiyayya da aka yi wa ‘yan Najeriya a kasar.

Naija News ta fahimta da cewa abin ya faru ne a ranar Lahadi, 8 ga Satumbar, bayan da jami’an tsaro suka yi artabu da masu satar kayakin mutane a cikin barkewar sabon rikicin.

7. Ex-AGF, Adoke ya Bayyana Manyan ‘Yan siyasar da suka Kusan tilasta shi da kisan kansa

Mohammed Adoke, tsohon Babban Lauyan Tarayya, kwanan nan ya bayyana cewa bayan ya bar ofis a shekarar 2015, ya kusan tunanin kashe kansa saboda zargin da aka yi masa.

Adoke yayin da yake magana kan bayyana mutanen da suka tsananta masa, ya anbacin Mataimakin Shugaban kasa, Yemi Osinbajo; mukaddashin Shugaban Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa, Ibrahim Magu; da Sanata Ali Ndume a matsayin wadanda ke bayan binciken sa da kalubalai.

8. Kotun Koli ta Tsige Memba Na Jam’iyyar PDP, Ta Bayyana Nasara Ga APC

Kotun daukaka kara ta Majalisar Dattawan Najeriya a Abakaliki, jihar Ebonyi a ranar Litinin din nan, ta yanke hukunci a madadin kungiyar All Progressives Congress (APC) dangane da Karamar Hukumar Ikwo \ Ezza ta Kudu.

Kotun a hukuncin da ta yanke, ta kori memba da ke wakiltar mazabar Ikwo \ Ezza na mazabar Kudancin tarayya, Lazarus Ogbee na jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP).

9. PDP Ta Mayar da Martani Bayan Lai Mohammed Ya Roki ‘Yan Najeriya da suyi wa Shugaba Buhari Hakuri

Jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) ta yi kira ga shugaban kasa Muhammadu Buhari da ya sauka daga shugabancin kasar nan da nan.

Babbar jam’iyyar adawar ta yi wannan kiran ne a lokacin da take mayar da martani game da wani faifan bidiyo da ke fitowa a kafafen sada zumunta inda Ministan yada labarai da al’adu, Alhaji Lai Mohammed, ya yi kirar hakuri ga ‘yan Najeriya kan takardar shaidar WAEC ta shugaban kasar.

Karanta kari da Cikakken Labaran Najeriya a shafin Hausa.NaijaNews.Com