Connect with us

Labaran Najeriya

Kasafin Kudin 2020 Zai Taimaka Wa Najeriya Zuwa Ga NEXT LEVEL – Osinbajo

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Shugaba Muhammadu Buhari ya samu yabo da karramawa daga Mataimakin sa, Yemi Osinbajo, kan saurin sanya hannu kan kasafin kudin shekarar 2020 zuwa doka.

Kamfanin dilancin labarai na Naija News ta ba da rahoton cewa Shugaba Buhari a ranar Talata, ya rattaba hannu kan kasafin kudi ta 2020 zuwa doka a Fadar Shugaban Kasa, Abuja.

Ka tuna da cewa Mataimakin shugaban kasar ya halarci lokacin rattaba hannu kan kasafin kudin shekarar 2020 da shugaban ya gabatar a fadar gwamnati.

Osinbajo yayin da yake magana kan kudirin dokar ya lura cewa kasafin kudin zai taimaka ga bunkasa kasar zuwa gaba.

Osinbajo wanda ya sanya a shafin sa na Twitter ya rubuta cewa, “Sa hannu a kasafin kudin shekarar 2020 a yau, Shugaba Buhari ya maido da tsarin watan Janairu zuwa Disamba.”

“Kasafin kudin zai taimaka ga bunkasar ayyuka “zai ciyar da kasar mu ga ci gaba yayin da muke zuwa Next Level.”