Manyan Labarai daga Jaridun Najeriya ta ranar Jumm’a, 27 ga Watan Disamba, Shekara ta 2019

Wadannan ne Manyan Labarai ta Jaridun Najeriya a yau Jumm’a, 27 ga Watan Disamba, 2019

1. Ayodele Ya Sanar da Annabcin 2020 A kan Buhari, Tinubu Da Sauransu

Wanda ya kirkiro cocin INRI Evangelical Spiritual Church, Oke-Afa, Ejigbo Lagos, Primate Babatunde Elijah Ayodele ya fitar da annabce-annabce na shekarar 2020 akan Najeriya da Shugaba Muhammadu Buhari.

Mashahurin malamin ya yi wahayin ne a yayin taron INRI Evangelical Church of Spiritual Church na shekara da shekara.

2. Bakar Ranar Kirsimeti A Ikilisiyar RCCG Yayin Da Fasto, Dansa Da Diyarsa Suka Mutu Cikin Ruwa

Gabriel Diya, Fasto na Ikilisiyar Cocin Christian Church of God (RCCG) da ke a kasar Landan da ‘ya’yansa biyu, sun mutu a wani wurin wanka a Costa del Sol, a kudu na Spain a Kirsimeti.

Naija News ta samu labarin cewa Fasto na RCCG din da ‘yarsa, Comfort Diya ‘yar shekara 9, da dansa, Thanks-Emmanuel Diya, dan shekaru 16, duk sun fada cikin wata tafki.

3. Atiku Na Iya Fita Don Takara Ga Zaben Shugaban Kasa A PDP,  Shekarar 2023 – Inji Shugaban BoT

Shugaban, kwamitin amintattu na jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP), Sanata Walid Jibrin, ya ce tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar na da ‘yanci don neman tikitin takarar shugaban kasa a shekarar 2023.

Da yake zantawa da manema labarai a birnin Kaduna, jigon a jam’iyyar PDP ya ce duk wani mai so da kuma ke da cancanci a jam’iyyar daga kowane bangare na Najeriya yana da ‘yancin neman tsayawa takarar shugaban kasa a tsarin sa.

4. ISWAP ta Kashe Mutanen Da Suka Sace A Ranar Kirsimeti Da bada Hujjoji

Kungiyar Islamic State West Africa a ranar Kirsimeti ta yanke hukuncin kisa ga wasu fursunoni goma sha daya, wadanda yawancinsu Kiristoci ne.

Ahmad Salkida, wani dan jaridar da ya shahara wajen sanya ido kan ayyukan ta’addanci ne ya sanar da hakan.

5. Ba a tsananta wa Kiristoci ba a Najeriya – Sultan ya gaya wa CAN

Mai Martaba Sarkin Musulmi, Sa’ad Abubakar, ya ce ya kadu matuka da ikirarin Kungiyar Hadin Kan Kiristocin Najeriya (CAN) na cewa ana tsananta wa Kirista a kasar.

Naija News ta ba da rahoton cewa kungiyar Kiristocin ta goyi bayan hada Najeriya a cikin jerin kasashen da suka amince da tafiyar da hidimar addini da Amurka ta saki.

6. Fadar Shugaban Kasa tayi bayanin Dalilin da yasa DSS ta saki Dasuki Da Sowore

Fadar shugaban kasa ta ba da dalilan da ya sa suka sa aka saki tsohon mai bada shawara kan tsaro (NSA) ga shugaban kasa, Sambo Dasuki da jagoran zanga-zangar #RevolutionNow, Omoyele Sowore.

Kamfanin dillancin labarai na Naija News ta ba da rahoton cewa, Ma’aikatar Tsaro ta kasa (DSS) a ranar Talata ta saki su biyun sakamakon umarnin daga babban lauyan hukumar kuma Ministan Shari’a, Abubakar Malami.

7. Gwamna Makinde yayi Magana akan Mutuwa Kafin Shekaru 30

Gwamna Seyi Makinde, Gwamnan jihar Oyo a ranar alhamis ya bayyana cewa yana tsoron kar ya mutu kafin ya cika karin shekaru 30.

Gwamnan jihar Oyo ya bayyana hakan ne yayin da yake jawabi a wurin bikin godiya don bikin zagayowar ranar haihuwarsa ta shekaru 52 a Ikilisiyar St Peter’s, Aremo, Ibadan, babban birnin Jihar Oyo.

Ka samu kari da Cikkaken Labaran Najeriya a Shafin Naija News Hausa