Connect with us

Uncategorized

2019: Farmaki ya tashi tsakanin APC da PDP a Runfar Zabe ta Jihar Kano

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Farmaki ya tashi a runfar zabe mai lamba 001 da ke a Wad na Chiranci, karamar hukumar Gwale da ke a Jihar Kano a yayin da dan takaran kujerar Gwamna daga Jam’iyyar PDP a Jihar, Abba Yusuf ya hade da Ciyaman na Jam’iyyar APC na Jihar Kano, Abdullahi Abbas.

Naija News Hausa ta gane da cewa ‘yan siyasa biyun sun jefa kuri’ar su ne a runfa daya. Farmakin kuma ta fara ne sakamakon yabo da kirari da mabiya bayan dan takaran jam’iyyar PDP ke yi ga dan takaran su. Da mamba jam’iyyar APC suka gane da hakan, sai suka fara jefe-jefen dutse har farmaki ya tashi tsakanin.

A halin yanzu ba cikakken bayanin yadda abin ta kare. Amma ka kalli bidiyon yanayin a kasa kamar yadda gidan jaridar Daily Trust suka bayar.