Connect with us

Uncategorized

Gbajabiamila ya gabatar da sabon jagoran babban Rukunin Majalisar Wakilai

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Kakakin yada yawun Majalisar Wakilai, Hon Femi Gbajabiamila ya gabatar da Ado Doguwa, dan majalisa da ke wakilcin Jihar Kano a karkashin Jam’iyyar APC, a matsayin jagoran babban rukunin Majalisar wakilai.

Naija News Hausa ta gane da hakan ne a sanarwan da Gbajabiamila ya bayar a yau Alhamis, 4 ga watan Yuli, anan birnin Abuja.

Haka kazalika aka gabatar da Mista Peter Akpatason, dan Majalisa daga Jihar Edo a karkashin Jam’iyyar APC, a matsayin mataimakin jagoran Majalisar.

Mun ruwaito a Naija News Hausa a baya da cewa Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai ya gabatar da sunayen mutane goma shadaya (11) ga Majalisar Wakilan Jihar Kaduna don amince da sanya su a kujerar Ministoci a Jihar.

Kakakin gidan Majalisar, Aminu Shagali ya bayyana sunayan mutanen da El-Rufai ya bayar a Majalisar.

KARANTA WANNAN KUMA; Tasirai da ke cikin ga Anfani da Namijin Goro da baka san da su ba.