Connect with us

Labaran Najeriya

A Karshe, Buhari ya Rattaba hannu ga biyan Kankanin Albashin Ma’aikata na naira 30,000

Published

on

at

Buhari Signing Minimum Wage Bill, Naija News Hausa, Hausa News, Labaran Hausa daga Naija News

Bayan jayayya da jita-jita hade da barazanar Ma’aikatan kasa game da kankanin albashi na naira dubu 30,000 da gidan Majalisai suka gabatar a baya, kamar yadda muka kuma sanar a wata sanarwa a Naija News Hausa.

Shugaba Muhammadu Buhari ya kai ga amincewa da kuma rattaba hannun sa da takardan dokan biyan kankanin albashin ma’aikata na naira dubu Talatin, kamar yadda aka aminta a baya.

Wanda ya biyo ne bayan da Gidan Majalisar Dattijai da Majalisar Wakilai suka amince da dokar da kuma sanya hannun su a kwanakin baya.

Naija News Hausa ta gane da cewa Ma’aikata a baya sun kara tunawa da kuma rokon shugaba Muhammadu Buhari da yin hanzari wajen rattaba hannu ga dokar kamin ranar 1 ga watan Mayu 2019, a yadda shugabancin kasar ta so a da.