Connect with us

Labaran Najeriya

Manyan Labarai daga Jaridun Najeriya ta ranar Talata, 14 ga Watan Mayu, Shekara ta 2019

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00
Manyan Labaran Jaridun Najeriya a Yau

Wadannan ne Manyan Labarai ta Jaridun Najeriya a yau Talata, 14 ga Watan Mayu, 2019

1. Gwamna Samuel Ortom ya gana da shugaba Muhammadu Buhari

A yau safiyar Talata, 14 ga watan Mayu, Shugaba Muhammadu Buhari yayi ganawar kofa kulle da Gwamnan Jihar Legas, Akinwunmi Ambode; Gwamnan Jihar Benue, Samuel Ortom da kuma Nasir El-Rufai, Gwamnan Jihar Kaduna, a nan cikin fadar shugaban kasa ta Birnin Abuja.

Anan ne Gwamna Ortom ya bayyana yanayi da mawuyacin hali da Jihar Benue ke a ciki ga shugaba Buhari.

2. Ganduje ya Mika Sandar Ikon Sarauta ga Sabbin Sarakan Kano

Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Ganduje, a ranar Litini da ta gabata, ya bayar da Sandar Ikon Sarauta ga sabbin Sarakai Hudu da ya nada a Jihar Kano.

Mun ruwaito a Naija News Hausa a baya cewa Gwamna Ganduje ya rabar da kujerar Sarautan Jihar Kano ga rukuni Biyar hade da wadda Muhammadu Sanusi ke jagoranta a da.

3. IGP ya nada sabon Ofisan karban ƙara

Shugaban Jami’an Tsaron ‘Yan Sandan Najeriya, IGP Muhammed Adamu, ya nada ACP Markus Ishaku Basiran a matsayin Ofisan da zai jagoranci rukunin karban kara, (Complaints Response Unit – CRU).

Yin hakan, ACP Markus Ishaku Basiran ya maye gurbin ACP Abayomi Shogunle, wanda aka mayar a matsayin sabon Area Kwamanda na yankin Nkalangi, a Jihar Ebonyi.

4. Za a Rantsar da Shugaba Buhari a hidimar lape ranar 29 ga watan Mayu

Shugabancin kasar Najeriya ta gabatar cewa za a rantsar da shugaba Muhammadu Buhari a matsayin shugaban kasan Najeriya a karo ta biyu, ranar 29 ga watan Mayu 2019.

Naija News Hausa ta fahimta da cewa hidimar zai kasance ne a lape, ba kamar yadda aka saba yi ba.

5. An tsige Sowore daga kujerar shugabancin Jam’iyyar AAC

Jam’iyyar Siyasa ta African Action Congress (AAC) sun gabatar da dakatar da Omoyele Sowore a matsayin Ciyaman na Tarayyar Jam’iyyar, hade da wasu kuma daga Jam’iyyar.

Naija News ta gane da hakan ne a wata sanarwa da Ciyaman na Kwamitin Jam’iyyar ya bayar a ranar Litini, 13 ga watan Mayu, 2019 a birnin Abuja.

6. “Na Karu ga Fahimta da Fasaha a yanzu” inji Ambode bayan da ya ziyarci Shugaba Buhari

Gwamnan Jihar Legas, Gwamna Akinwunmi Ambode, a wata ziyarar da yayi ga shugaba Muhammadu Buhari ranar Litini da ta wuce, ya bayyana cewa ya karu da fahimtar lamarin siyasa a shekaru hudu da yayi a kujerar shugabancin sa a Jihar Legas.

Ambode ya fadi hakan ne a wata ziyarar da ya kai ga Fadar shugaban kasa, anan birnin Abuja don nuna godiya ga goyon baya.

7. Ba zani sake neman zabe ba bayan shekarar 2023 – Ekweremadu

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattijai, Sanata Ike Ekweremadu ya bayyana da cewa ba zai kara neman takara a gidan Majalisa ba idan ya gama wakilcin shi a shekarar 2023.

Ya bayyana hakan ne ga manema labarai a ranar 12 ga watan Mayu, a wajen hidimar murnan ranar haifuwa da cika shekaru 57 da yayi.

8. Dalilin da ya sa Hukumar EFCC ke binciken Saraki – Sagay

Ciyaman na Kwamitin Shawarwari ga shugaban Kasa, Farfesa Itse Sagay, ya bayyana da cewa Hukumar EFCC na binciken Bukola Saraki ne akan wasu tarin dukiya da yayi a hanyar da bata dace ba.

Naija News Hausa ta fahimta da cewa EFCC, a makon da ta gabata sun dakile gida da dukiyar Sanata Saraki da ke a shiyar Ikoyi, a Jihar Legas.

Ka samu kari da cikakken labaran Najeriya a shafin Hausa.NaijaNews.Com