Connect with us

Uncategorized

Kalli dalilin da yasa Gwamnatin Jihar Zamfara ta dakatar da Sarakai biyu a ranar guda

Published

on

at

Gwamnatin Jihar Zamfara ta dakatar da Sarkin Maru, Alhaji Abubakar CIKA Ibrahim da wakilin kauyan Kanoma, Alhaji Ahmed Lawal da zargin hada hannun da ‘yan ta’adda a Jihar.

Naija News Hausa ta gane da hakan ne bisa wata sanarwa da aka bayar daga hannun Alhaji Yusuf Idris, darakta Janar na sadarwa ga Gwamnan Jihar, a jagorancin sabon gwamnan Jihar, Alhaji Bello Matawalle.

Gwamnatin Jihar ta tsige ‘yan sarauta biyun ne bayan zarge-zarge da alamar da aka gane da su na hada kai da ‘yan hari don aiwatar da mumunar hali a yankin.

A haka kuma aka bukacesu da barin kujerar wakilcin su da kumar mikar da gurbin ga wasu har sai an gama bincike kan zargin.

A fahimta da ganewar Naija News Hausa, bisa rahotannai da tarihi kuma, a karamar hukumar Maru inda aka tsige masu sarauta biyun ne mahara da bindiga suka fara kai hari a kauyan Langido a shekarar 2011 da ta shige a baya.

Ka tuna da cewa a baya kuma, tsohon gwamnan Jiahr, Alhaji Abdul’aziz Yari da tsige ‘yan sarauta shidda a Jihar a lokacin da yake kan jagoranci.

Naija News Hausa ta ruwaito a baya da cewa rundunar Sojojin Najeriya sun harbe mutane biyu a wata farmaki da ya tashi a yayin da tulin mutane ke wata zanga-zanga a shiyar Gurin, a karamar hukumar Fufore ta Jihar Adamawa.

Wannan ya faru ne a yayin da mutanen yankin sun fita zanga-zanga akan rashin amincewa da umarnin hana amfani da babura da jami’an tsaro a goyon bayan gwamnatin jihar ta gabatar da shi.