Connect with us

Labaran Najeriya

Shugaba Buhari Ya Bar Daura Zuwa Jihar Kaduna A Yau

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Shugaban kasa Muhammadu Buhari a yau Talata ya bar garin sa Daura, cikin jihar Katsina bayan kammala ziyarar kadamarwa ta aiki ta kwanaki biyar.

Naija News ta rahoto cewa Buhari ya bar Daura ne da safiyar ranar Talata kuma ya sauka a Filin jirgin saman Umaru Musa Yar’Adua akan helikofta.

Shugaban ya samu karban marabta daga Gwamnan jihar Katsina, Aminu Masari; Mataimakinsa, Mannir Yakubu, da Shugaban Majalisar Dokoki ta Jiha, Tasi yake Maigari.

Sauran wadanda suka marabci shugaban sun hada da Sakataren Gwamnatin Jiha, Dakta Mustapha Inuwa; Shugaban Jam’iyyar APC ta reshen jihar Katsina, Shitu Shitu; da Alkalin Kotun jiha, Mai shari’a Musa Danladi, da Shugabannin Ma’aikata na Jiha da membobin Majalisar zartarwa ta Jiha.

Daga nan, jirgin saman shugaban kasan ya tashi daga tashar jirgin sama da misalin karfe 10:23 na safe zuwa jihar Kaduna inda ake sa ran zai halarci taron Babban Hafsan Sojojin shekara da shekara.

Naija News Hausa ta ruwaito a baya da cewa Shugaba Buhari Ya Kadamar Da Bude Sabon Makarantar Jami’ar Sufuri A Jihar Katsina

A ranar Litinin din da ta gabata ne Shugaba Buhari ya yi bikin bude makarantar jami’ar sufuri a Daura, inda kuma ya jagoranci bude hanyar Kwanar Gwante, wacce ke kan hanyar Kano zuwa Daura.

Kalli Hotuna a kasa;