Connect with us

Uncategorized

Kungiyar ‘Yan Shi’a Ta El-Zakzaky Sun Halarci Coci Da Bayar da Kyautannai A Ranar Kirsimeti

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Wakilan Harkar Musulunci a Najeriya (IMN), wadanda aka fi sani da Shi’a a ranar Laraba sun halarci hidimar coci ta Kirsimeti a wasu sassan arewacin Najeriya.

A cocin daban daban na Advent, Samaru, Zariya, jim kadan bayan kammala hidimar, shugaban kungiyar, Farfesa Isa Hassan-Mshelgaru ya ce muhinmancin halartar wannan hidimar shine inganta soyayya, hakuri da fahimta a tsakanin yan Najeriya.

Naija News Hausa ta ruwaito a baya da cewa wasu ‘yan Bindiga Sanye Da Kayan Sojoji sun sace yara uku na Mista Obi a Jihar Kaduna

Mugun yanayi ya sanya wani dan kasuwa a Kaduna, Christian Obi kuka da hawaye a ranar Alhamis bayan da wasu ‘yan bindiga sun sace yaransa uku.

Mutumin yayin da yake zantawa da manema labarai a gidansa da ke Sabon Tasha, Kaduna, ya ce ya ga wadanda suka sace yaran ne sanye da kayan sojoji a cikin gidansa amma sai ya shiga buya.